BABI NA SHA SHIDA

2.4K 126 0
                                    

*SANGARTA*

                        ©
            *ZULAYHEART RANO*

       *Sadaukarwa ga Khadija s Muhammad my Cittah*

*Alhamdulillah Ina godiya da Allah ya kawo mu wannan lokaci, ina son in dakata da typing wannan littafin har sai Allah ya kaimu bayan sallah lafiya, ina wa ɗauka cin musulmai murnar zuwan wannan wata mai alfarma Allah ya sada mu da Alhairin da ke ciki Ubangiji ka bamu rabauta da falalar da ke wannan wata na Ramadan*

_*Har lau dai korafi baya karewa? To duk kuyi hakuri Yar Mutan Rano tana kara ce wa kuyi hakuri ku kara akan na da, insha Allah bayan sallah ba za ku yi korafin rashin typing ba*_ i heart you irin totallyn ɗin nan😍😍

                      *16*
Nannauyan ajiyar zuciya ya sauke, tare da zubawa Ameesha ido cikin wani irin yanayin da shi kaɗai ke gane wa, cikin taushin murya ya ce

"Magana ta tasa ki kuka?"

Girgiza kai ta yi , ba tare da ta ce komai ba.

"No Maryam in muna magana ki rika buɗe baki Please."

"Ni fa Dr ba maganar ka ta sani kuka ba." A shagwaɓe ta karasa maganar.

Ji ya yi ta bala'in burgeshi,yana ɗaya daga cikin abin da yasa yake sonta kenan.

"To me ya saki kuka in ba maganar ba, na ce  baki min Allah ya sanya Alhairin Aure na ba, sai na ga kin fara kuka ko?"

Harara ta watsa masa ta ce

"Ni fa kaina ke ciwo shi ne kawai."

"Hmm Maryam kenan kina da saurin daukar zafi, nifa banga abin tada hankali ba cikin abin nan, in ki ka bi a hankali to komai zai ta fi yadda ki ke mafarkin samu."

Ya yi maganar ta re da kashe mata ido ɗaya.

Saurin ɗago da kai ta yi tana kallon sa, tare da mamakin maganar da ya faɗa "kenan ya san tana sonsa?" Ta yi saurin kawar da tunanin don ta san ba haka ya ke nufi ba.

Mik'ewa ta yi tare da ɗaukar jakarta, ta kuma kallon kyakkyawar fuskasa ta ce

"Dr ni kam zan wu ce don yamma na yi."

Wani tsadadden murmushi ya bata, wanda ya kara wa fuskarsa kyau ya ce

"To Princess sai yaushe kenan?"

"Gobe school zan shiga sai zuwa jibi."

"Ok Allah ya kaimu, mu je na saukeki ko kin zo da mota ne?"

Wani irin daɗi ya ziyarci zuciyar ta , amma sai ta fuske ta ce

"A'a Dr ka barni kawai na hau nafef."

Ta ida maganar tana tafiya.

"Maryam." Ya kira sunan ta da wani irin murya.

Cak Meesha ta tsaya ba tare da ta juyo ba, don yadda ya ambaci sunan sai ta ji kamar duniya babu wanda ya iya fadar sunan kamar shi.

"Mu je na ce maki ko?"

Ya yi maganar yana daukan key.

"Dr ai baka duba petient na ka ba?"

"Dama ba su nazo gani ba, da abin da ya kawo ni, kuma na gani hankalina ya kwanta."

Yana bata amsa ne yana rufe kofar, a tare suke jerawa sun yi mugun da ce wa da juna, don duk wanda ya gansu sai ya yi tunanin miji da mata ne a haka har zuwa inda motarsa ya ke , buɗe mata kofa ya yi ta shiga sannan shima ya zaga.

Yana shiga wayar sa ta soma ringing, da sauri ya dauko don ganin me kiran ɗan murmushi ya saki tare da karawa a kunne

"Hello My Anee ya aka yi?"

SANGARTA COMPLETEWhere stories live. Discover now