TALATIN DA SHIDA

2K 109 0
                                    

*SANGARTA*

  
                        ©
           *ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*


    *Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*

Dedicated to _*RAHEENAT MAMOUDOU (HEENART)*_

'''Betsy Allah ya baki lafiya, jin ciwon ki nake kamar a jikina yake 😭😭 sosai na yi missing ɗin ki, Allah yasa kaffara ne'''👏
                      *36*

Nenne bata ce masa komai ba, sai ma zama da ta yi tana jiran zuwan Ameesha, bata fi minti biyar ba ta dawo da ganin yadda ta turo baki zaka san da magana, kusa da Nenne ta zauna cikin zallar SANGARTAR da ta saba.

        " 'Yata lafiya kuwa?"
 
        "Ba Abba bane wai inzo in tambayi Dr, idan ya bari sai mu tafi." Cike da shagwaɓa har da dira kafa kamar wata karamar yarinya ta ida maganar.

Wani irin murmushi Dr ya saki don tabbas ya ji dadin maganar Abba, ya kuma bashi wani matsayin na musamman, domin ya cika suruki na gaske.

Sosai ta cika da mamakin furucin Abba da ya ce sai da izinin Dr zata fita, to wani matsayi Dr ke da shi a wajenta da har Abba zai fadi wannan maganar?" Tambayar ta yiwa kanta wanda bata da amsar sa, ko kafin ta lalubo amsa sai jin maganar Nenne ta yi.

       "To kai ka ji abin da ta ce ko?" Babu alamar dariya Nenne ta masa tambaya.

       "Eh! Na ji Nenne a dawo lafiya, mu je nima ina son k'ara ganin garin."

Kusan a tare suka fito, domin su Meena ma yawon zaga garin zasu je, haka suka fita suna hira Ummi da Nenne suna taɓa hira, Meena da Meesha ma haka, sai su Jaheed da Dr, sun zaga gari sosai har sayayya suka yi, Dr ma ya sayawa Aneesa tsaraba domin ya faranta mata, washe gari jirjin karfe takwas suka bi.

              *NIGERIA*

ko da jirgin su ya sauka kowa gidan sa ya nufa, Dr dai kin bin su Nenne ya yi domin cewa ya yi sai ya kai Ameesha har gida, Allah ya sani baya son rabuwa da ita don dai ya zama dole ne.

Yana cikin gidan sai wajen karfe shida ya fita, a lokacin tuni Aneesa ta shirya masa lafiyayyen girki, shi kadai take jira ganin har shida ta yi sai ranta ya soma ɓaci domin ta yi amanna yana tare da Ameesha shi yasa ya manta da ita.

Sallama ya yi tare da shiga cikin falon, Aneesa dake zaune ta watsa masa wani irin kallo tare da dauke kai

       "My Anne mai nayi kuma daga dawowata?" Ya yi maganar tare da hugging ɗinta.

Bata fuska ta yi ta turo baki, tana mutsu-mutsu so take ta zame jikinta daga rikon da ya mata

      "Sorry na yi laifi ko? Amma fa ba laifi na yi ba, kinsa tare da mara lafiya nake dole tana da buk'atar kulawa."

    Kuka ta fashe masa da shi tana faɗin.

      "Ai Ni bana buk'atar kulawa tunda har ka tafi kusan kwana goma." Da shashsheka take maganar.

Gyara rikonta ya yi ya ce

       "Please ki yi hakuri bazan kuma ba, kin ji matata farin cikina?"

      "Babu komai ya wuce."

      "Da gaske?"

      "Eh! Mu je ka yi wanka sai ka ci abinci."

     "Yawwa matata yar albarka."

Aneesa ta taimaka masa ya yi wanka, jallabiya ya zira lokacin ana kiran sallar magriba, masallacin kofar gidan ya je lokacin da ya dawo bai taras da ita a falo ba, don haka sai ya nufi bedroom ɗinta, zaune ya ganta gaban dressing mirror tana fesa turare, shakar kamshin ya yi yana rungume ta jikinsa.

SANGARTA COMPLETEWhere stories live. Discover now