TALATIN DA BIYU

2K 112 1
                                    

*SANGARTA*


©
*ZULAYHEART RANO*
My Wattpad username
*ZulayheartRano89*


*Sadaukarwa ga Khadija S Muhammad My Besty*

'''Sadaukarwa ga AMRAH AUWAL MASHI (Princess Amrah) na sadaukar maki da wannan page din kyauta domin jin dadin ki, Allah ya kara basira da kaifin k'wak'walwa, ki ci gaba da suburbuɗo mana AMRAH NAKE SO muna jin dadin buk ɗin sosai, ina gaida RAZ'''

_*I hearttttt You My Besty irin har abada dinnan.*_💞
*32*

Tsayuwar motarsu ta yi dai dai da zuwan motarsu Abban Ameesha, cikin sauri Dr ya faka motar ya fito, kai tsaye wajen su Abba ya nufa, cikin fara'a Abba ya fito tare da mikawa Dr hannu sukai musabaha, ya yi da Dr ya tsuguna yana gaida Ummi da Abba cikin kunya.

Wasu motar ce suka kuma shigowa, yaya Jaheed ne da matarsa sai ta ya Abdul da Meena, duk fitowa suka yi suka nufi inda Alhaji Taheer ya ke.

Sai a lokacin Haydar ya fito daga cikin motar su Abba, gaisuwar mutunci suka yi da Dr sannan suka kama hanyar falon, wanda tuni Aneesa ta shiga tana zaune a falon tare da Nenne suna dan taɓa hira.

Sallamar Dr ce ta katse masu hiran "Nenne ga su Abban Ameesha sun iso fa." Dr ya yi maganar bayan sun gama gaisawa.

"Je ka dakin Bobbo ka sanar masa, bari na shigo da su Hajiya Halimar." Nenne ta ida maganar tana mik'ewa.

Daret Dr bed room na Bobbo ya shiga ya sanar masa da zuwan su Alhajin, a tare suka fito fara'a sosai Bobbo ya saki suka gaggaisa da Alhaji Taheer, don tuni sun shiga falon.

"Nenne ina Meesha ne?" Meena ce ta yi tambayar don tun shigowar ta bata ganta ba.

"Twin's din Ummi har kin gaza hakuri kenan? To tashi tana cikin bedroom." Cikin dariya Nenne ta yi maganar.

Ai tun kafin Nenne ta rufe baki har Meena ta nufi bedroom din.
Su dinma dariya suka yi, suna jin dadin yadda Meena da Meesha suke rayuwa, sam babu hassada balle bakin ciki.

Dr kallon agogon hannunsa ya yi yana faɗin

"Abba time yana tafiya fa, 7:45 AM yanzu kuma 8:15 AM jirgin zai tashi."

"To mai muke jira? Ya ci gaba "ai inaga gara mu tashi mu tafi kar mu makara." Abba ya gama maganar dai dai da fitowar Meena da Meesha. Murmushi Abba ya saki ganin Ameesha.

Ita kam wajen Nenne ta nufa ta zauna, sai kallon su Ummi take yi, ido Aneesa ta zubawa Ameesha tana kallon kyau irin na Ameesha sai yau ta yi mata kollon sosai. Sanye take da wani hadaddiyar doguwar riga kalar pink da white, fuskarta ta sha kwalliya daga inda Aneesa ke zaune tana jiyo sansanyar kamshi turaren da ke jikin Ameesha a jiyar zuciya ta sauke a ranta ta ce "Dole Hamman ka riƙa yin rawan kai."

Shi kuwa Dr tunda yaga Ameesha ta fito sai ya maida hankalinsa kacokan kan Ameesha yana kallon irin kyau da ta yi, yana jinjina k'ok'ari irin na Meena don yasan aikinta ne wannan. Sosai ya shagala har ya manta a wajen da yake sai da ya ji muryar Alhaji Taheer yana faɗin

"Dr ka tashi mana lokaci fa yana tafiya."

"To." Dr ya faɗa yana mik'ewa.

Gaba daya suma suka mik'e, daret wajen motoci suka nufa kusan duk bakin su dauke da addu'ar samun nasara, kai tsaye babban filin saukar jirgin saman suka ɗauki hanya, cikin mintina ƙalilan suka isa airport.

Ba su wani daɗe ba, suka gama duk wani shiga da fita har komai ya kammala, sai jiran a fara kiran fasinjoji Dr ne ya dubi Abba ya ce

"Abba zamu tafi a yi mana addu'an samun nasara." Cikin ladabi ya yi maganar.

SANGARTA COMPLETEWhere stories live. Discover now