chapter 63

287 32 0
                                    

(¯'*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*´¯)

      *🌹HAR ABADA🌹*
          *(bazamu rabeba)*

       *LOVE &* *FRIENDSHIP*

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/

TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09

  
Follow me on Wattpad @ayeeshatmuhd

         *RUBUTAWA*

        *UMMU NAJMA*
   
*DEDICATED TO*
*MAMAN MAMY SHALELE AND BEELAT SARAUNIYA*

63🍎

Tana zaune a gaban table tana karatu a system dinta, gaba Daya ta canza tayi fresh hasken fatar ta ya qara fitowa, Amman har yau da damuwa shinfide a kan fuskarta.

tana iya qoqarin ta wajen ganin ta rage tunani ta saka karatun ta a gaba amman wani lokaci yin hakan yakan gagare ta, takan zauna ita kadai tayi ta kukan rashin ya Imran memories dinshi sun zamo Mata abokan rayuwa ko abinci take ci sai ta tuna shi, Yanda yake rayuwar shi abin burgewa ko yaushe fuskar shi dauke da murmushi gashi yasan Kan mace shugaba ne a fannin soyayya uba na gari Mai qoqarin bawa yaran shi ingantaccen tarbiyya, she just missed him so much.

Qarar wayarta ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da talula, ganin Wanda take Kira yasa ta saki murmushi tayi picking hade da fadin
"Afuwan best yauma nayi laifi, Yaya gida Yaya babana da baby Raheema"

Qwafa Feenah tayi ta gyara kwanciyar ta jikin Ahmad dake faman rubuce rubuce ta Hana shi sakat tace

"Ai wallahi na kusa na daina Kiran ki, kiyi ta min iskancin da Kika ga dama Kinga Ina kula ki ne Amman gobe idan Baki Kira kin gaisa da yaran ki ba bazan sake neman ki ba, kuma su kawai Kika sani ba Zaki  tambayi Yaya Abdallah na yake ba ko?"

" Baiwar Allah saurin me kike yi ai shi gaisuwan shi na musamman ne, Amman Yaya banji kukan Raheema ba ko ta daina rikici ne?"

" Ina kuwa? Ta koma wurin mom ne ana koya Mata tafiya yanzu sai na wuni zubur ban saka ta a idona ba har na fara maida qiba na wallahi"

" Wato Kun maida iyayenku masu raino ko? Haka ma Sahar ta dauki safiyya ta bawa Ammi raino shiyasa aihuwa bayi Muku wahala ai"

"To Yaya zakiyi damu? Nifa shiyasa banison Kiran ki sai ki yita ma  mutum qananun mita yanzu ma babana ne ya Dame ni na Kira mishi momy Yana so ya Miki lissafin abubwan da Zaki kawo mishi idan Zaki dawo"

" Kai wannan baban namu babu dama har yafi Abdallah kwadayi ko dayake ya dauko kamannin uwarshi akwadaisu ai idan baiyi kwadayi ba Sai a tambaye shi"

" Dakata malama kada ki nemi ki zage ni, babba dani ne kike cemin kwadayayya Dan kin raina ni? Ko bakisan ni maman wasu bane? Kina ganina Kai harda furfura na Tara manyan sojoji masu ji da qarfi Wanda zasu Kama Meenal su nada Mata na jaki amman kice Ina kwadayi?"

Dariya Eesher tayi tace
" da qarya aka miki?"

Har cikin ranta taji dadin dariyan da ta saka ta ko yaushe tana son ganin aminiyarta cikin farin ciki, taci gaba da cewa
" To wallahi ki kiyaye ni ko yanzun nan natura babana Bauchi wurin momy idan ya kama kunnen Shaheeda hmm sorry ganda, Yanda kike ganin shi dan qarami ya iya cizo haqwaran shi kaman reza dazun nan ya kafa ma sageer ya gudo neman tsira Kuma na boye abuna"

HAR ABADA (Under Edition)Where stories live. Discover now