🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
*ZYNAH*
_(An Interesting love story 2017)_
By Aisha Muhammad ( Mzz Daddy 💋)
*Happy Sallah to all Muslim Ummah Allah ya maimaita mana Ameen thumma Ameen*INTRODUCTION :- Ni Aisha Muhammad (Mzz Daddy 💋)
Sabuwar writer ce wanda wanna novel din shine first novel dina , da fatan readers zasu bani hadin kai. Allah yasa mudacè (Ameen)DEDICATION :- I dedicate dis novel to ASY KHALEEL cos if nt for u i won't make here.ILYSVM💋💋
WARNING :- Ban rubuta wannan story din dan cin zarafin wani ko wata ba, in kunga labarin yayi kama life style din wani ko wata toh kuyi hakuri kumin afuwa akasi aka samu.
GODIYA :- Ina godiya ga Allah (S W T ) da ya bani iko da kuma basiran rubuta wannan littafi.
QUOTE :- No matter who u ar or wat ur work is, u need to nurture ur relationship . Make sure u schedule time for d well being of ur relationship .
0⃣1⃣
Lagos state, 12:27pmMota ce kirar venza fara take tafiya a hankali har ta kai wani makeken gida dake cikin Banana Island Lagos,horn takeyi da karfi ba sassautawa har saida mai gadi yazo ya bude mata gate din ta shiga tayi parking a parking lot din gidan,fitowa tayi daga motan fuskanta dauke da murmushi mara misaltuwa tayi cikin gida da gudun ta tana ihun Daddy! Daddy!! Daddy!!!
Wanda take kira Daddy ne ya sauko daga stairs dinda ke parlour din yana cewa mamana lafiya irin wannan kira haka,ai se ki kashe min dodon kunne,shawagbe fuska tayi tace ni na isa in kashe ma dodon kunne ai..........bata karasa fadan abunda takeso tace ba wata mata wanda nakesa ran itace mahaifiyar ta tace *ZYNAH* wai yaushe zaki girma ne kin shigo gida da ihu ko sallama bana tunanin kinyi.
Momsie yi hakuri wallahi dadin da nake ciki yanzu ne yasa nayi behaving hakanan amma amin afuwa bazan karaba. Toh shikenan an miki afuwa inji momsie a yayinda take neman zama kusa da Daddy dake zaune a three sitter dinda ke parlour,toh momsie nagode.
Daddy,momsie ta kirasu duk suka juyo suna Kallonta tare da bata full attention dinsu dan jin me zata fada,nan tace musu albishirinku?daddy yace goro, tace fari ko ja?momsie tace fari kal kal kal,nan tace musu ta samu admission a A B U Zaria nd she's going to study the course she's being dreaming of which is medicine. Daddy ne yace wow dats my gurl ai nasan u can do it saboda i trust u.
Momsie kam baki bude take kallon ýa da uba yanda suke wani jindadi dan kawai ta samu admission. Islah kallonmamanta tayi murmushi dauke a fuskanta tace momsie baza kice komai ba koh u ar nt happy about my achievement ne. Ajiyan zuciya momsie tayi sannan tace yanxu Islah fisabillihi bazaki iya cigaba da karatun ki a nan Lagos ba sai kinje chan uwa uba wata duniyan da ba dangin iya bare na uba, ba mai kula dake Eh ?
Nan take murmushin dake fuskanta ya gushe,cikin sanyin murya tace momsie baki yarda dani bane koh baki yarda da tarbiyyan da kika bamu ba? At least if u won't encourage me don't discourage me, all i need is your trust and prayers momsie dats all i need tafada a yayinda kwalla ke neman zubowa daga idonta saboda ta lura kaman mamanta na kwankwanto a kanta kuma abunda ke bakanta mata rai kenan.
Kinga *ZYNAH* bawai ban yarda dake bane ko kuma ban yarda da tarbiyyan da na baki bane a'a kawai dai ka haifi ďa ne baka haifi halinshi ba shine, abunda nake tsoro shine kije ki hadu da kawayen da zasu gurbata miki tarbiyyan da nayi shekara goma sha bakwai ina baki amma............bata karasa maganan ta ba Islah ta katseta da cewa dats it, i knew it, kawai kice baki yarda dani ba amma ba komai nagode tafada a yayinda ta tashi ta bar musu parlourn ta haura sama zuwa dakinta.
Meyasa zaki gaya mata irin wannan maganan, Daddy kenan yakema momsie fada akan abunda tacema ýarsa da yakejin sonta har cikin bargon jikinshi saboda mai sunan mahaifiyarshi ce. Momsie kasa cewa komai tayi dan tasan abunda zai biyo baya kenan saboda ta fada ma Islah gaskiya ita kuma tayi fushi har da zubda kwalla .
Daddy ne yaci gaba da cewa yarinyar nan ko tayi karatu anan ko batayi ba indai Allah ya nufa tarbiyyan ta zata gurbace bawai fata ba dole ta gurbace tunda ba wayon mu bane zai hana gurba cewanta ba, sai anan momsie tasamu bakin magana tace, toh Alhaji Allah ya baku hakuri ya huci zuciyarku kuma in sha Allah zanje naba Islah hakuri akan abunda nafada mata amma dan Allah kadaina daga mun murya bana jin dadin hakan wallahi. Cikin sanyin murya yace alamun ya sauko yace toh aike dince wani sa'in saida daga murya, tace afuwan,murmushi sukayi gaba dayan su sannan yajawo abarshi a jiki tareda mata alkawarin ya daina daga mata murya,cigaba da hiransu sukayi. Sallama sukaji atare suka amsa momsie tace auta har kuntashi tace eh momsie kinsan mun fara exams dats y.
Momsie tace toh sai aje a cire uniform dan nasanki yanzu zaki iya cewa sai kinci abinci tukunan. Daddy ne yace toh ai ba'a wasa da ciki koh auta? tace ai kuwa dai sannan tace ina Islah momsie tace tana dakinta,tace ok sannan ta haura sama da niyyan zuwa dakinta amma tana kaiwa dai dai kofan dakin Islah sai taji sheshekar kuka wanda hakan yasata yin sallama tareda shiga dakin. Mamaki ne ya kamata ganin yayarta kwance rufe da ciki a kan makeken royal bed dinta tana kuka, cikin sauri ta karasa tareda zama kusa da yarta tace my sister lafiya kike kuka meyasa meki?
Ai kuwa nan da nan tayi shiru tareda dagowa tana kallon kanwarta sai kuma ta rungumeta tare da dasa wani sabon kukan tana cewa ISLAM momsie batayi trust dina ba bata yarda da tarbiyyan da tabamu ba tunda gar tana tunanin inaje School zan lalace indinga yin abunda naga dama tunda ba idon kowa a kaina, dagota tayi daga jikinta bayan ta gama sauraren ta da kuma lallashinta har tayi shiru sannan tace my sister wa yace miki momsie bata yarda dake ba, meyasa kikace haka, saboda..........nan ta kwashe labarin komai tafada mata, ajiyar zuciya Islam ta sauke sannan tace momsie ta yarda dake 100% saidai ba ita kadai ba kowace uwa dole taji wani iri ganin ýarta mace zata wani garin da batasan kowa ba karatu, u ar mistaken kuma kin fassara maganan ta the other way round ba haka take nufi ba hope u understand, nan ta kada kai alamun ta gamsu da maganan kanwarta kuma tayi dana sanin gayawa momsie magana da tayi sannan tayi alkawarin zataje ta bawa momsie hakuri.
Nan tama kanwarta godiya data fahimtar da ita tareda da tambayanta meyasa ta dawo da wuri? nan take cemata saboda sun fara exam ne ,tace hakane exam din second term koh, tace eh tareda mikewa zata bar dakin,nan ta juya ta tambaye ýarta ko taci abinci tace a'a,toh bari na cire uniform sai muje dinning, *ZYNAH* tace ba matsala sannan ta fita tayi nata dakin tabar ýarta da tunani kala kala akan university life........
Shin idan *ZYNAH* ta tafi school karatunta zata sa a gaba ko kuma wani abu daban ❓
Ku biyo ni nan gaba dan jin yanda zata kaya. ..
YOU ARE READING
ZYNAH
Mystery / ThrillerHere is a story of a teenage hausa girl Zynah who happens to come from a wealthy nd peaceful family but was hated by her younger sister whom she loves a lot, nd betrayed by her bestfrnd whom she tells all of her secret, nd unknowingly fall for a gu...