🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
*ZYNAH*
(An Interesting Love Story 2017)
By Aisha Muhammad (Mzz Daddy 💋)
QUOTE:- "Just because the past didn't turn out like you wanted it to, doesn't mean your future can't be better than you ever imagined".
_I dedicate dis page to my other half, my partner in crime nd lastly my one nd only trublsum sisto *Halima aka me hancin shovel*😅 Allah ya nuna min aurenki musha budiri.😜
1⃣2⃣
Layi na kaiwa kansu suka shiga Admin office din suka karba admission letter dinta sannan suka wuce bank dinda ke cikin school din biyan kudi. Koda suka shiga bank din akwai layi, Uncle Yusuf ya duba agogon hannunshi kirar Rolex yaga uku da rabi harda en mintina se yace mata " Kinga *BEAUTY* zumu wuje gobe in mun dawo se mu biya kudin amma yanzu lokaci ya wuce" ta bata fuska kaman tayi kuka tace " Uncle dan Allah mujira" be damu da yanayin ta ba yace "kalla tym,kuma laifin waye,nake ne,ke kika saura kina bacci har lokaci ya wuce, yanxu zaki wani ce mujira a Karfe nawa kikeso layi yazo kanmu" narai narai tayi da ido kaman tayi kuka tace "toh shikenan Allah ya kaimu goben" ya amsa mata da "ameen" sannan suka fito ya juya wurin Ashanty data makale mai kaman chewing gum (taga fyn boy lol) yace "Toh madam Ashanty mu zamu wuce amma gobe zamu dawo saboda akwai sauran aiki a gaban mu. So, se munzo gobe kenan ko" fuskan ta dauke da murmushi ga baki yaki rufuwa kaman gonan auduga tace "Allah ya kaimu, amma dan Allah in kunzo gobe kamin waya maybe u will need my help in one way or d other, tunda ni school din ba bako na bane","ok zan nemeki se goben, bye","bye" suka wuce, basuyi nisa sosai ba ya juyo yaga har yanzu tana nan inda ya barta bata ko motsa ba ,se ya daga mata hannu tareda kashe mata ido daya aikuwa tayi suman tsaye tana kallon bayanshi harya bace mata.
Suna zuwa bakin titi suka samu taxi suka shiga tareda fada mai inda ze kaisu, sun fara tafiya *ZYNAH* ta kalli Uncle dinta tace "Uncle it seems u ar fond of dat Ashanty,ko itama zaka mayar da ita girlfrnd dinka","uhmmm nima tunanin da nakeyi kenan after all she's beautiful,ko baki ganta ba doguwa ga kyau ba laifi gata da dan haske kinga yakamata in samu budurwa anan garin, ko me kika gani","nidai Uncle a tunani na ka kyaleta saboda she's still a student,yanzu take 300 level karka raba mata hankali gida biyu" yayi shiru ya tunanin maganan niece dinshi can yace " shikenan zanyi yanda kikace" taji dadi sosai ganin ya karbi shawaran ta hannu bibbiyu tace " dats my Uncle" tareda bashi high five. Haka sukaci gaba da hira har suka kai hotel dinsu suka biya me taxi suka wuce ciki kowa yayi dakinshi.
Wanka tayi tareda alwallah tayi sallahn la'asar dayake sunyi azahar a school sannan tasa evening gown me spaghetti hands ta zauna a kan gado tareda dauko waya har zatayi kira taji cikinta na kugi alaman yunwa, se alokacin ta tuna duk wannan budirin da suke tayi a school bataci abinci ba banda soft drink da cake din da Uncle ya matsa mata yace se taci wanda cake dinma bata iya taci ba drink din kawai tasha. Se ta tashi tasa wayanta charji ta dauki karamin veil tasa sannan tafita taje dakin Uncle Yusuf tasa meshi kan sallaya shima yanzu ya idar da sallah yace mata "Ya akayi *BEAUTY*" tace "Uncle yunwa nakeji","me zakici" tace "anytin" nan ya dauki intercom din dakin ya musu order din fried rice with chicken da chips da exotic drink, cikin 10min aka kawo musu two plate kowa ya dau nashi amma *ZYNAH* duk wannan yunwan da takeji bataci ya kai spoon goma ba tace ta koshi amma ba laifi taci chips din , dama Uncle yasan za'a rina yace seta kara ko five spoon, da kyar ta kara ya kira aka kwashe plates din ita kuma ta kuma dakinta ta dau wayarta ta kira Bestee dinta ta video call suka sha hira suna fadama juna hw much dey miss each other, suna gama wayan ta kira Islam amma ba'a dauka ba, se da ta kira kusan so biyu a na ukun ne aka dauka tace "Islam ina kika ajiye waya inata kira","na shiga toilet ne, ya kike ya registration din kun soma" ," eh mun soma dazun ma munyi waya da Momsie wai kina school","eh ta fada mun,wai kunyi waya da Daddy ma","eh munyi,so ya kike ba wani matsala a gidan ko","babu, zan kiraki later Momsie na kirana" bata jira me zatace ba ta kashe wayan a zuciyarta tace "kece matsala na dukda kinyi tafiya amma har yanzu Daddy beda zance se naki, i wish u neva come back"(wata sabuwa inji en chacha). Itama *ZYNAH* ajiye wayan tayi tareda kwanciya wanda ko minti goma ba'ayi ba bacci ya dauke ta saboda gajiya.
**********
Su *ASHRAF* sundawo daga open day inda suka sha complain kala kala akan Juwairiyya saboda shegen tsokana irin nata, sun dawo ya sauke Sameer gida sannan shima ya karasa cikin gida, yana shiga direct part din Ummi ya shiga ya same ta a kitchen itada Minal da yake rannan girkinta ne yayi sallama suka amsa yace "Ummi naje school din dawowa na kenan","yayi kyau, me teacher dinsu tace?" ,"teacher dinsu Husna tace she's very intelligent nd neat kuma tana da respect amma tana makeup in zatazo school saboda haka ta dena,nasu Juwairiyya kuma inji teacher dinsu wai tana kokari amma batajin magana akwai ta da tsokana" Minal tace "Ai dama Husna akwai son kwalliya na mata magana har na gaji" Ummi ta karba da cewar bari so dawo duk zan sasu a gaba in musu fada sosai","Ummi ni zanje na huta","kaci abinci ne","a'a amma banjin yunwa","toh a huta lfy" ya fita zuwa bangarensu,sukuma sukaci gaba da aikinsu.**********
Yau ya kama Tuesday wanda *ZYNAH* tun da asuba data tashi bata koma barci ba gudun karta makara irin na jiya, by 8 duk sun shirya suka tafi school din,suna zuwa suka biya kudin saboda ba layi sosai, suna biya suka fito Uncle yakira Ashanty saboda ta nuna musu coordinator's office,ba jima se gata sukayi en gaishe gaishen su tayi leading dinsu zuwa office din aka mata signature sannan akace su dawo gobe saboda HOD dinsu baya nan kuma suna bukatan signature dinshi. Haka suka hakura amma ran Uncle ya baci saboda alla alla yake sugama abunda ya kawosu su koma saboda akwai aikin da ke jiranshi amma dole su hakura. Haka suka koma hotel din dan su samu hutu itako *ZYNAH* waya ta dauko tana buga _Candy crush_ dan ita hankalin ta kwance ganin sunkusa gama abunda ya kawo su.**********
Sameer ne ya shigo dakin *ASHRAF* amma baya ciki sedai da alamun yanzu gama drawing ya tashi daga wajen, zuwa yayi kusa da sketch board din se yaga mace ce a garden tana zaune da littafi a hannun ta da alamun karatu takeyi sedai yanda ta yafa veil dinta yasa ba'a ganin fuskan ta. Yana cikin nazari hoton *ASHRAF* ya shigo dakin Sameer yace "guy nice drawing" murmushi kawai yayi tareda cewa "She was in my dream again last night, i think she's trying to pass me an information" Sameer yayi dariya yace "nd wat if ba mutum bace aljanah ce" *ASHRAF* ya harare shi yace" Allah ma bazesa inga aljanah ba" shidai Sameer bece komai ba in banda dariyan keta da yake mishi._Kuyi hakuri da wanna ba yawa_
_Mzz Daddy 💋✍🏻✍🏻_
YOU ARE READING
ZYNAH
Mystery / ThrillerHere is a story of a teenage hausa girl Zynah who happens to come from a wealthy nd peaceful family but was hated by her younger sister whom she loves a lot, nd betrayed by her bestfrnd whom she tells all of her secret, nd unknowingly fall for a gu...