. 🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
*ZYNAH*
(An Interesting Love Story 2017)
By Aisha Muhammad (Mzz Daddy 💋)
QUOTE:- "When one door of happiness closes, another opens; but often we look so long at d closed door that we do not see the ones that has been opened for us".
_I dedicate dis page to my lovely niece *Ummima*_
0⃣5⃣
Sun isa shagon suka shiga da sallamansu , babban shago ne sosai komai na ciki mai tsada ne , Zee Mama na ganinsu ta taso ta tarbesu ta fara'anta suka gaisheta ta amsa tareda basu wurin zama suka zauna sannan ta umarce en aikinta dasu kawo musu abunsha , nan aka kawo musu drink da ruwa suka sha . Zee Mama ta tambayesu me suke bukata Humaira tace "gown mukeso","wani iri"? " me kyau dai" cewar *ZYNAH*. Nan ta dauko wani sabon jaka wanda bata ma soma siyar da kayan ciki ba amma kasancewar su regular customers ne yasa ta fito musu dashi. *ZYNAH* ce ta soma duba kayan taga duk latest design ne basu yi common ba, nan ta dauko wata arniyar fitted gown wanda bayan yafi gaban tsayi kadan sai wurin tommy din ana sa abortion belt saboda masu tumbi . Tana dauko wa Humaira tace " wow amma gown dinnan yatafi da imani na gaskiya yayi", Zee Mama nawa"? Murmushi tayi dan tasan duk wanda yaga gown din dole yasoshi sannan tace" 15k ne ba tsada","kawo biyu dan nima inaso yamin kyau"...
Ta musu package dinshi tabasu suka biyata suka mata sallama suka fita, suna fitowa *ZYNAH* tace "dan Allah bestee mu biya shoprite akwai abunda nakeso na siya","kedai ce kinason kisiya chocolate","nidai muje kinji plss","toh muje". Nan suka yi Ikeja city mall saida Humaira taje tayi order din pizza da humburger sannan suka shiga ciki *ZYNAH* kam ba wani abun arkizin da ta siya sai kayan zakin da take ta kwasa har saida Humaira tamata magana , sun biya kudi sukaje suka karbi pizza dinsu suka kama hanyar gida. Suna isa gida sukaga Islam a dinning ita kadai tana cin abinci,"My sister kun dawo tun dazo na dawo daga school banganki ba Momsie tace min kun fita","eh wlh mun siyo gown ne","sis Humaira me kika kawo min"? "Pizza da humburger na siyo","yehhh kaman kisan burger is my favourite .
Dariya suka yi saboda yanda ta react tareda zama baje baje a kasa suka fara cin pizza banda Islam da tamayar da hankalin ta kan burger sai kwakolo kayan jams dinda ke ciki takeyi, "Ina Momsie batasan mun dawo ba"cewar *ZYNAH*" ta fita wai mijin kawarta ya rasu taje ta'aziya","ehyya Allah ya jikanshi"Ameen duk suka amsa . Sallaman Uncle Yusuf sukaji suka amsa suka mishi sanda zuwa ya amsa musu" Islam ina Momsie","taje gidan rasuwa","waya rasu"?"mijin kawarta",
"Allah ya jikanshi "Ameen", remote ya dauka ya chanza channels din zuwa CNN yana kallon news *ZYNAH* ce tace "Uncle bismillah" dan Humaira kunyarshi takeji yace mata "a'a kuci kayanku ni na koshi,Daddy ya min magana wai zan rakaki Zaria registration","eh ai ran Sunday zamu tafi","haka yace, kinfara shiri","eh nafara","gud ni zanshiga ciki na huta" ya tashi ya tafiyanshi. Suna gama ci Humaira tace"ni zan wuce gida saboda lokacin Islamiyya yayi , da nasan zan dade dana dauko uniform dina","ok y nt kisa nawa ","kai swthrt ai jikinmu ba dayaba ","ok sai mun hadu a islamiyya".Nan suka rakata har ta wuce sukama suka koma ciki kowa yayi dakinshi dan shirin islamiyya.Sallah sukayi suka shirya, Islam ce tafara gamawa sannan ta shiga dakin *ZYNAH* taga bata gamaba"yi sauri sister kar mu makara","ai nagama muje",saida ta cika jakanta da chocolate da sweets tabawa Islam wani sannan suka wuce. Driver ne ya kaisu islamiyyan inda suna kaiwa Islam ta wuce ajinsu aji uku, *ZYNAH* kuma ta tsaya bakin gate tana jiran zuwan Humaira dan kullum haka sukeyi wacce tafara zuwa zata jira yar uwarta. Tayi Kusan 10mins sannan Humaira tazo, saida suka rungume junansu dan murna kaman ba dazu suka rabu ba sannan suka wuce ajinsu aji shida. Ana tashi islamiyya kowaccen su ta wuce gida cike da kewan juna .
Haka raywarsu ke tafiya cike da so da kaunar juna.
Shin haka rayuwar wannan family da kawayen zaici gaba kubiyo ni dan jin yanda zata kaya ........
Kuyi hakuri da wannan ba yawa yau banjin dadi ne
Mzz Daddy💋 ✍🏻✍🏻
YOU ARE READING
ZYNAH
Mystery / ThrillerHere is a story of a teenage hausa girl Zynah who happens to come from a wealthy nd peaceful family but was hated by her younger sister whom she loves a lot, nd betrayed by her bestfrnd whom she tells all of her secret, nd unknowingly fall for a gu...