🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
*ZYNAH*
(An Interesting love story 2017)
By Aisha Muhammad ( Mzz Daddy 💋 )
*Ina mai baku hakuri akan wani kuskure da akasamu a page one , zakuga wani wurin na rubuta Islah instead of Zynah Dan Allah kuyi hakuri typing error ne, kuma kaman yanda na fada muku ni sabuwar writer ce shiyasa such mistake are likely to happen. Tnx for understanding nd d cooperation ILYSM* ❤
QUOTE:- Don't interrupt, even if u need to put ur hands over ur mouth to stop urself. Learn to fight fairly. No name calling. Don't make threats, Apologise wen u knw u should. If u'ar too angry to really listen, stop ! go into another room, take space for urself, breath nd calm down.
Remember : ur partner is nt d enemy._I dedicate dis page to my one only sister *Halima ( limsyberry)*_
0⃣2⃣
*ASALINSU*
Alhaji Sani Mai Dala da Hajiya Hasiya sune iyayen Alhaji Muhammad Sani Mai Dala. Wanda shine da daya tilo agurinsu, saboda haka suka dauki son duniya suka daura masa, baya taba neman abu gurin iyayen shi ya rasa dukda ba wani arziki bane dasu ba saidai muce rufa asirin Allah. Alhaji Sani yasamu lakabi da Mai Dala ne saboda tun yana yaro beda burin da ya wuce inya girma yazama mai kudin da Naira ma baze dinga rikesu ba sai Dala, saboda haka abokansa suka sa mashi Mai Dala wanda idan suka kirashi da sunan wani dadi yakeji kaman ance ga kujeran makka nabaka.
Haka sunan ya bishi dukda Allah bai nufa zaiyi irin wanan kudin ba. Alhaji Sani ya kasance da kasuwa inda yake siye da siyarwa a cikin garin kano wanda nan ne garinsu kuma tushensu. Cikin ikon Allah kasuwan cinsa ya fara bunkasa har yana tunanin fara fita gari gari saro kaya amma Allah bai nufa ba saboda wani mummunan hatsari daya samu akan wani bridge wanda nan take yace ga garinmu rai yayi halinsa (saidai muce Allah ya jika shi da rahama Ameen).
En uwa da abokan arziki ba wanda baiji mutuwan bawan Allahn nan ba saboda mutum ne shi mai son jama'a da barkwanci. Bayan anyi arbain aka raba gado inda tilon danshi wato Muhammad ya tashi da kusan duka abunda mahaifinshi ya bari inda cikin hikima da dabara shima yaci gaba da gudanar da kasuwancin mahaifinshi.
Cikin ikon Allah komai yazo mishi da sauki inda kasuwancin sa yasamu karbuwa har yarafa fita gari gari kaman Lagos da Port Harcourt, ganin kasuwancin ya bunkasa sosai yasa ya samu yaran aiki yasa a karkashin sa wanda duk wata yana biyansu albashi mai tsoka. Kasuwanci ya karbeshi sosai inda ayanzu har kasashen ketare yana zuwa amma iyakanshi Africa .
Cikin yawon kasuwancin sa ne yahadu da matarsa wato mahaifiyar *ZYNAH* a Ethiopia inda yaje wani business meeting daya last for one month, toh a dan zaman da yayi achan ya hadu da ita a wani restaurant dinda yake zuwa cin abinci wanda iyayen tane masu restaurant din amma ita ke managing din wurin. Tun zuwanshi na farko ya hadu da ita wanda nan take yanemi nutsuwarsa ya rasa . Da haka ya koma hotel dinda ya kama amma yakasa tabka komai sai tunanin kyakyawar fuskar budurwar da yagani a restaurant yakeyi.
A haka ya wuni ya kwana ranan suku suku dashi, washegari yana gama abunda yakeyi ya koma restaurant din nan yasameta yafada mata abunda ke tafe dashi wanda hannu bibbiyu ta karba tayinshi suka sasanta tsakaninsu , kafin ya koma Nigeria sukaje wurin iyayenta da maganan wanda da kyar da tsidin goshi suka yarda dan basa so ýarsu tayi nisa dasu. Da haka ya dawo gida ransa fari tas, yana dawowa yama mahaifiyarsa maganan inda ba bata lokaci taje wurin dangin mahaifinshi da maganan suma suka amince ya biya ma en uwan mahaifinshi uku kudin jirgi dashi hudu akaje aka nema mai auren Aisha masoyiyarsa inda cikin wata biyu akayi aurensu aka bashi matarsa sukazo gida Nigeria inda ya ajiyeta a gidan mahaifiyarshi kafin ya kammala ginin da yakeyi a Lagos .
Ya kammala gininsa yanemi mahaifiyarsa tabisu su tare tare amma fir taki wai ita bazata bar gidan da mijinta yagina ta gumisa ba, ba yanda suka iya haka suka barta tare da samu mata mai aikin da zata dinga taimaka mata. Da haka suka tare shida matarsa inda suke zaune cike da soyyaya , amince , yarda , da kuma girmama juna . Sunyi shekara uku ba haihuwa amma ba wanda ya taba jinkansu haka mahaifiyarsa ma bata damu ba saboda tasan cewa Allah ne mai bayarwa , a shekara na ukun ne ta samu ciki Wanda cikin ikon Allah cikin na cika wata tara tahaifi ýarta mace kyakyawa son kuwa kin Wanda yarasa , ranan suna yarinya taci sunan mahaifiyar Alhaji Muhammad Mai Dala wato Hasiya amma ana kiranta da *ZYNAH*( abu mai kyau in other words kyakyawa) , tun daga lokacin Alhaji Muhammad ya dauki son duniya ya dorawa ýarsa saboda Mai sunan mamansa ce kuma tana kama da matar sa.
Tun lokacin basu kara haihuwa ba sai bayan wani shekara ukun sannan suka sake samun mace inda yarinya taci sunan Mahaifiyar Aisha Wato Maryam amma suna kiranta da *ISLAM*(Peace) .Tun daga kanta haihuwa ya tsaya ma Aisha saboda haka suka dauki son duniya suka dura masu amma mahaifinsu yafison *ZYNAH* kuma agaban kowa nunawa yakeyi Wanda hakan yasa *ISLAM* bata sakewa dashi sosai tafi sabawa da mahaifiyar ta , dukda yanda yake nunamusu banbanci na bakanta mata rai amma bata taba nunawa ba .
Wannan kenan
Back to story line............
*Karku gaji da biyoni saboda akai abun tausayi , al'ajabi , kunya da kiyayya a cikin wannan novel din.*
_Keep following so u won't miss_
*Mzz Daddy💋* ✍🏻✍🏻
YOU ARE READING
ZYNAH
Mystery / ThrillerHere is a story of a teenage hausa girl Zynah who happens to come from a wealthy nd peaceful family but was hated by her younger sister whom she loves a lot, nd betrayed by her bestfrnd whom she tells all of her secret, nd unknowingly fall for a gu...