🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
*ZYNAH*
(An Interesting Love Story 2017)
By Aisha Muhammad (Mzz Daddy 💋)
QUOTE:- "Some people pass through our lives in a shorter time frame than we had hoped to teach us things they never could have taught if they stayed".
_I dedicate dis page to my lovely nd beautiful niece *AFRAH(hukuman babanta)* Allah ya raya min ke swthrt yasa naga aurenki nan da shekaru masu zuwa (lol), i hrt u gurl❤._
1⃣1⃣
Yau ya kasance Monday kuma ranan da *ZYNAH* zata fara registration dinta amma saboda son jiki irin na *ZYNAH* ba ita ta tashi ba se past 10 dan se da Uncle yazo ya tashe ta sannan ta tashi a gurguge ta fada bathroom shikuma ya girgiza kai ya fita cikin zuciyanshi yace "bansan randa yarinyar nan zata canza ba,indai haka zataci gaba da wannan shegen barcin nata toh kuwa tanada jan aiki nan gaba" haka yata zancen zuci har ya kuma dakinshi ya dauko laptop dinshi yana wani aiki da zaman banzan da zeyi yana jiranta.
Wanka tashiga tayi brush tayi alwallah ta fito daure da towel daure a jikinta da kuma wani karami tana goge jikinta dashi, tana gama goge jikinta ta shafa mai da powder da lipstick sannan ta taje gashinta sannan taje wurin akwatinta ta dauko wani skinny jeans red tasa da white top an rubute _I'm sexy_ da red ink a jiki sannan tasa hijab har kasa tayi walha tayi addu'ointa sannan ta cire hijab din ta dauko long after dress fari me transparent tasa da veil dinshi, sannan tasa flat baby shoe da bag red ta dauko duk wani important document dinda tasan za'a bukata irinsu birth certificate ,indigene form weac nd jamb result, primary nd secondary school certificate da application form duk tasa a wani file sannan tasa su ajakanta neatly saboda karsu hargitse ta fito tareda daukan duk abun bukatan ta (including sweets i guess).
Dakin Uncle Yusuf tashiga da sallaman ta ya amsa batare da yadago ba tace " Uncle na gama" seda ya rufe laptop dinda ke gabanshi sannan ya taso ya matso kusa da ita tareda rike mata kunne yana murdawa a hankali yanda baze mata zafi sosai ba sannan yace "next tym ki bari in rigaki gamawa ina zaman jiranki" ta rike hannunshi da ke kan kunnen ta tace "sorry Uncle, nima bansan lokaci ya wuce ba amma next tym zansa alarm" se alokacin ya saketa yace "sleeping sickness" kunne ta murza tana turo baki, be kulata ba yayi gaba ta bishi a baya suka wuce.
Gaban hotel din suka tsaya da yake kan titi hotel din yake har suka samu mai taxi Uncle Yusuf yace "dan Allah ABU zaka kaimu" dan taxi din yace "yallabai wanne? na Samaru ko na Kongo" se ya jiyo ya kalli *ZYNAH* da take tsaye ta kallon masu wucewa yace mata "Samaru ne ko Kongo" tace "Uncle Samaru ne" sannan ya juya yace ma dan taxi din "Samaru ne" yace " kutaho muje" duk suka shiga bayan motan drivern ya mika titi sai Samaru .
**********
*ASHRAF* ne zaune a dakinshi yasa sketch board a gabanshi yana drawing yana gamawa sega Sameer yashigo da sallama *ASHRAF* ya amsa sannan Sameer ya kai dubanshi kan sketch board din yace " bros yaushe rabonka da drawing" *ASHRAF* yace "na dade","amma wannan fa, i thought kace zaman drawing na bata maka lokaci shiyasa ka dena" *ASHRAF* yayi ajiyan zuciya sannan yace "haka ne, amma jiya nayi mafarkin wata yarinya zaune a kusa da swimming pool tasa kafanta cikin ruwan ta juya min baya ga gashinta ya zubu a bayanata da rabin fuskanta wanda hakan yasa bansamu daman ganin fuskanta ba. So, da safe nan kuma senaga na kasa manta mafarkin dats y i decide to draw d girl who knows one day i might meet her" ya karasa zancensa da murmushi a fuskansa , Sameer yace "I see , but wat if she's d one u saw yesterday","wace wannan kuma" Sameer ya kalle shi yace "wanda kabani labarinta jiya, ta airport" tsaki *ASHRAF* yayi yace "ni wlh na manta ta" cike da mamaki Sameer yake kallonshi sannan ya daure yace "bros ar u for real, da gaske kake kodai wasa kakeyi","da gaske nake mana" shidai Sameer shiru yayi yana mamakin abokinshi yanda kwata kwata he is nt fond of girl ba ruwanshi da harkan mata, ace mutum ya hadu da ita jiya har yana cewa ta burgeshi amma a kwana daya har ya manta, lalle lamarinshi ya girmama. *ASHRAF* ne ya katse mai tunani tareda cewa "guy bari na shirya ka rakani school dinsu Husna wai yau suke open day kuma Ummi tace naje musu, yanzu in banje ba Juwairiyya zata iya kai karana wurin Abba dan ba kunya gareta ba" Sameer yayi dariya yace "Juwairiyya rigima duk girman mutum bata kunyan kai karanshi","ai Abba ke daure mata gindi har tasamu fuskan kai kara" ya fada sanda ya mike ya ajiye sketch board din gefe sannan ya wuce wardrobe tareda dauko black jeans da T-shirt brown yasa wanda ya kwanta a fatan jikinshi sannan suka fita.**********
Sunkai Samaru ya sauke su a first gate din Uni din Uncle Yusuf ya ciro 1k ya ba dan taxi din, har zasu wuce dan taxi din yace "yallabai tsaya ka karba canji" Uncle Yusuf yace "ka rike kawai","toh toh toh nagode nagode" haka yata godiya Uncle Yusuf ya daga mishi hannu yana murmushi sannan ya kama hannu *ZYNAH* suka shiga ciki "Uncle dan sake min hannu kar ayi tunanin ko am still a kid" dariya yayi ya sake mata hannu sannan yace "da ke mecece har yanzu ina miki kallon wannan small gurl dinda ta girma a gabana me kukan sweet" baki ta turo tace Uncle "ni din" yace "eh mana" sukaci gaba da tafiya tanata kallon makarantar a zuchiyarta tace "My dream school, Allah kasa nayi achieving abunda nazo nema a school dinnan"(nima na tayata da cewa Ameen). Tafiya sukeyi se kuma Uncle Yusuf ya tsaya yace " muna ta tafiya bamusan admin office ba,bari muyi tambaya" suna tsaye sega wata budurwa tazo wucewa Uncle Yusuf yace "excuse me" ta juyo fuska kadaran kahadan amma tana ganin Uncle Yusuf sai ta saki fuska ta washe hakora (taga haddaden guy) tace "yes, hw may i help u" shima murmushi yayi dan ya dago da ita sannan yace "dan Allah tambaya nake inane admin office" tace oh am going same way muje kawai" yace "dats gud" suka bi bayanta "by d way wats ur name" wani dadi taji tace "My name is Aisha but people call me Ashanty" yace "Aisha dats a nyc name nd more over my sisters name","is dat so , am glad dat i share d same name wit ur sis" haka yata janta da hira har suka kai admin office din *ZYNAH* na bayansu tana kallonsu ta girgiza kai chan kasa kasa tace "da kisan waye Uncle dina da baki saki jiki da shiba" suna zuwa admin office din suka taradda mutane zazzaune kowa na jira layi ya kai kasanshi " *BEAUTY* zauna nan bari na samo miki wani abu kici","no Uncle barshi banajin yunwa" dama yasan bata damu da abinci ba shiyasa be damu kanshi ba ya juya wurin Ashanty wacce ta makale mai taki tafiya sukaci gaba da hira har sukayi exchanging contact itakuma *ZYNAH*zama tayi tana chatting tana shan kayan zaki, in tasha wannan tasha wancan wa'anda ke zaune wurin se kallonta suke wasu na koda kyanta wasu kuma na mamakin yanda take ciye ciye , haka sukata zama har layi yazo kansu._Kuyi hakuri nasan nayi alkawarin zanyi typing dayawa yau amma rashin enough ba3 yasa na saba alkawari amma in Allah ya yarda gobe zanyi me yawa._
_Mzz Daddy 💋✍🏻✍🏻_
YOU ARE READING
ZYNAH
Mystery / ThrillerHere is a story of a teenage hausa girl Zynah who happens to come from a wealthy nd peaceful family but was hated by her younger sister whom she loves a lot, nd betrayed by her bestfrnd whom she tells all of her secret, nd unknowingly fall for a gu...