🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
*ZYNAH*
(An Interesting Love Story 2017)
By Aisha Muhammad ( Mzz Daddy 💋)
QUOTE:- "Love is an untamed force. When we try to control it, it destroys us. When we try to imprison it, it enslaves us. When we try to understand it, it leaves us feeling lost and confused."
_I dedicate dis page to *Khadijah (Mzz Adam)* Allah ya bar miki shi ya raya miki Ammatullah, wit much luv , i hrt u swthrt❤._
1⃣0⃣
*ZYNAH* ce kwance tana so tayi bacci amma ya gagara saboda tunanin *ASHRAF* da ya cika mata kwakwalwa, se tambayan kanta take meyasa takasa manta shi? meyasa inta rufe ido shi take gani? meyasa takasa samun sukuni duk tunanin shi ya addabeta? haka ta dinga tambayan kanta questions kala kala amma amsansu ya gagareta har sarkin sata ya saceta wato bacci.
*******
"Guy wai lfy yau gabadaya ka canza magana ma wuya yake ma" cewar Sameer ganin yanda abokinshi yayi sanya magana ma bayason yi daga uhm se uhm uhm "lfy lau nake me ka gani","gani nayi u look doll kaman sumtin is bordering u"," ba abinda ke damuna kawai dai i am nt in d mood ne" hummmm, ajiyan zuciya Sameer ya sauke tareda dafa kafadan *ASHRAF* sannan yace "look, kasan we've being frnds since childhood koh" *ASHRAF* ya daga mishi kai alamar "eh" sannan yace "gud, saboda haka u cannot tell me dat u ar alright nd u expect me to believe, kallo daya ze nuna min u ar nt alright, so just tell me wat d hell is bordering u" wani dogon numfashi *ASHRAF* ya ja sannan ya sauke ya kalle Sameer sannan kuma ya maida kanshi kasa tareda cewa " der is a gurl i meet today at d airport nd she was lyk" se kuma yayi shiru yana tunanin abunda ze ce Sameer yayi sauri yace " wow wow wow , guy don't tell me u ar in luv , so finally i've got to see dis day" *ASHRAF* ya hade giran sama dana kasa yace "yaushe nafada maka sonta naked da har zakayi jumping into into conclusion, well for ur information i don't luv her, i just lyk one of her characters ,i mean her confidence, saboda it seems lyk tanada confidence sosai nd kasan ina lyk din mace me confidence dan irinsu baza'a iya cutansu ba","well tunda kace haka so b it , let's change d topic" nan suka canza zancen suka koma hiran ball har akayi la'asar sannan suka tashi.*ASALINSU ASHRAF*
Alhaji Sagiru Fillo ya kasance fulanin Maiduguri ne gaba da baya shiyasa ake mai lakani da dan Fillo. Yanada mata biyu Maryam (Ummi) da Rukayya (Ammi) suna zaune cikin so da kaunan juna ba wani nuna kishi da sauransu. Ummi nada yara uku Kamal, Jamal da Hafsa sanda aka auro Ammi se haihuwan ya koma musu kaman competition inda Ammi ta haifi Fahad da shekara daya Ummi ta haifi *ASHRAF* ta kuma haifan Minal sannan Ammi ta haifi Basma Da Haydar se Ummi ta haifo Husna da auta Juwairiyya tunda daga lokacin kuma haihuwa ya tsayama dukkansu amma in kana zaune gidan bazaka taba gane wannan ne dan wane ba harse an fada ma saboda kamanni da shakuwa.Alhaji Sagiru Fillo ya kasance politician ne dan har ya kai ga yana neman matakin Governor amma aka dinga bashi warning kan lalle ya ajiye wannan post din amma yaki har abun ya kaiga aka fara barazanar kashe iyalinshi amma still yayi kunnen uwar shegu yaci gaba da campaign. Ana cikin haka akayi kidnapping first born dinshi Kamal, suka nemeshi har na tsawon kwana biyu amma babushi ba alaman shi, a ran kwana na ukun ne akaga gawanshi a wulakance kan titi wanda Alh Sagiru ya tabbata ba kowa ne ya mai wannan danyen aikin ba se competitors dinshi na wurin siyasa wanda wannan incident dinne yasa siyasa ya fita ranshi gabadaya har be sha'awan zama garin Maiduguri kuma, saboda haka ya yanke shawaran canza garin zama. Yayi shawara da matanshi inda suka yanke zama a Zaria wanda wannan dalilin ne yasa suka kuma Zaria da zama.
Doc Jamal wanda shine babba yanzu yayi aure da yara biyu mace da namiji, babban doctor ne yana zaune da iyalinshi a Lagos, se Barrister Hafsa itama tayi aure da ďa daya tana zaune a Abuja, se Fahad wanda he is 25yrs yanzu kuma yake service year dinshi amma ba'ayi posting dinsu ba tukun Accounting ya karanta kuma kusan shine ya fita zakka a family din saboda shaye shaye dukda baya shan sigari saboda baya son warin amma daga abunda ya kama codeine,tramol,rephnoyl anan kudinshi ke karewa,iyayenshi sunyi fada har sungaji suna rakashi da addu'an shiriya, se *ASHRAF* wanda he is 24, gentle guy ne beda rawan kai ko kadan ga rashin son magana dayawa amma indai yana cikin family dinshi ko yana tareda Sameer zeyi fira sosai amma bayansu dashi da bebe daya suke shiya course mate dinshi suke cewa yanada girman kai, se Minal wanda she is 22 nd a free girl ga fara'a amma batason karatu saboda haka ma da tagama secondary kin zuwa university tayi da kyar aka lallabata taje poly inda ta karanci Food science yanzu haka ta gama school ta shiga catering school shima ta gama tayi bead work shima tagama yanzu tailoring take koya , ita da *ASHRAF* 5 & 6 ne sun shaku sosai dan baya boye mata komai, in abu na damunshi itace abokiyar shawaran shi, se Basma wanda she is 20 , tana year two dinta a school inda take karantan Mass Communication akwai girman kai da nuna ita er manya ce, ba kowa takema magana ba se takama,se Haydar wanda he is 17, yanzu yake processing admission dinshi a _Oxford university,_shi kowa nashi yanada barkwanci da son mutane amma akwai shakiyanci, se Husna she is 12, yanzu take Jss2 uwar iyayice itama kaman Basma ce ta haifo ta halinsu daya shiyasa tasu ta daya , se Juwairiyya autansu kenan she is 6, ita primary 2 take akwai tsiwa da surutu ga iya kai kara gurin Abba ko kallon banza ka mata se ta maka ka a kotun Abbanta (lol). Wannan shine takaitacen tahirin gidansu *ASHRAF*.
_Muje zuwa_**********
Ba ita ta shi daga barci ba se 5:30 tana tashi taje tayi alwallah tayi la'asar sannan ta dauko wayanta ta fito zuwa dakin Uncle Yusuf ta iskeshi yana kallon _Teen Wolf_ a laptop dinshi "Uncle" jin an kirashi yasa jiyo tareda cewa "Na'am , *BEAUTY* ya akayi kina bukatan wani abune","a Uncle","me kikeso fada min","Uncle so nake mu fita mudan zagaya gari na gaji da zama wuri daya" ,"bari na gama kallon episode dinnan se muje" cike da jin dadi tace " Thanks" sannan ta koma dakinta ta dauko Kimono ta dora kan kayanta tafito, shima har ya shirya suka fito suna ta zagaya gari suna ganin yanayin arewa har magrib Uncle Yusuf yasiya musu San Yoghurt da cake suka koma hotel dinsu dansu huta, sunyi sallolinsu sannan tayi wanka tasa pink night gown iya gwiwa tasa socks dogo saboda sanyi sannan taje ta kwanta tareda jan comforter ta dauko wayanta tana karanta karanta English novel a wattpad _The Demon's soul_ har barci barawo ya saceta.
Se muce "duk nisan dare gari ze waye"_Kuyi hakuri da wannan nasan be dayawa Insha Allah next page zanyi shi dayawa_
_Mzz Daddy 💋✍🏻✍🏻_
YOU ARE READING
ZYNAH
Rejtély / ThrillerHere is a story of a teenage hausa girl Zynah who happens to come from a wealthy nd peaceful family but was hated by her younger sister whom she loves a lot, nd betrayed by her bestfrnd whom she tells all of her secret, nd unknowingly fall for a gu...