JADWA 26

62 3 0
                                    

Haka ya cika gaba da tafiya bai waiwayo ba nan mamaki ya kashe ko wa ita ko umma dadi far a ranta hidaya zatayi hauka, nan lantana taje ta jawo ta tace jadwa ya isa haka mu tafi daki muje mu dauka hijab mu rufe ma hajiya jikin ta sai suka juya suka wuce daki. Ita ma umma barin wurin tayi tafiya sai kuka su A'isha suka ja ta suka wuce part insu ba dun radiyar taso ba, shi ko Abba koda ya koma daki ya rasa abunda ke mashi dadi ya rasa gane ganshi kwata kwata wai meke faruwa ne abunda yake tambayen kanshi kenan sai gumi yake yi ita umma sai kallon shi take yi tana jiran yayi wani magana amma shuru ya kasa cewa komai.

Koda lantana da jadwa suka fito da hijab in da kyar suka iya sa mata shi a jiki da ihu ta cigaba da yi tana fisge fisge sai da rabi ta taimaka masu sannu suka iya rufe mata jikin ta sai faduwa take yi tana tashi duk ta rauna ta kanta abun tausayi nan jadwa ta wuce daki ta dauko wayan ta ta kira zainab.

Tana kiran zainab ta fada mata hankali ta ya tashi tace gata nan zuwa minti 20 tayi sai gashi ta iso da motor itama ganin hidaya a haka sai da hankalin ta yayi mummunan tashi. Tambayar jadwa take yi ina Abba ku? Sai ta nuna mata da hannu alamun yana part in umma da gudu ta je ta yi knocking in door shiru ba'a bude ba tayi ta bugu amma shiru da karfin da Allah ya bata ta turo door in yana budewa ta shiga sai sallama take yi taji shiru koda ta shiga bedroom umma ce ta gani da Abba kwance saman gado suna kiss. Nan tace wa'izubillahi ta fita sai umma tace lafiya dawo mana ya zaki zo ki bata mana jin dadin mu.

Aiko nan zainab ta gama fadan maganganu son ranta, tace umma kiji tsoron Allah wlh ko nayi rantsuwa bazan yi kaffara ba ina da sa hannun acikin al'amarin mommyn jadwa, ke wata irin azzaluma ce wai mai ta maki ne kin zo kin aure mata miji kin hana ta zaman lafiya, kinyi na farko baki ci nasara ba yanzu kin sake yin wani bazaki taba gama lafiya ba wlh kiji tsoron makomar ki nan umma tace uban wa ya fada maki ni ce nayi mata wani abu ? Dama ina da kishin ruwan ki wlh shi mijin ta gashi nan bai iya tsayawa wajen ba sai Ni? Ai shi ma ai alamu ya nuna ba yaya bane kin je kinyi mashi nashi sai Allah ya saka mana ace maki bamu san abinda kike yi bane, nan umma tace idan kika kara zagina sai na marai ki mara kunya kawai shi ko abba yana zaune kamar wawa yana kallon su shi dai gashi nan bai ma san me ke faruwa ya rasa gane kansa duk yadda umma tayi dashi yau haka ya ke biye mata.

Rikici dai ya kaure har sai da zainab ta kasa hakuri ta yanka ma umma mari, Aiko nan Abba ya tashi har jikin shi yana rawa ya yanka ma zainab mari ita ma yace ko don na kyale ki yanzu ki fita mun gida daga ke har hidayar tunda uwan ki ce idan ma jadwa zata biki ne duk bana bukatar ku, zainab hawaye wani na bin wani tana yaya Ni ce fa yaya meke faruwa da kai? Yaya me akayi maka? Yaya yaya...

Yace kar ki sake kiran suna na fita mun daki plsss aiko nan ta fita tana kuka mai tsanani duk abunda ke faruwa kan ido jadwa ne koda ta fito haka suka rungume kuka suna kuka mai tsanani sunfi minti goma a haka can lantana tazo ita da rabi suna lallashin su lokacin ko hidaya duk jikin ta ya fashe saboda faduwar da take yi duk yayi jini fuskan ta hauka dai teburan..

Ana cikin haka zainab ta gama kuma idon ta duk suka kumbura sosai ta dauki wayan ta ta kira dadyyn marwan ta fara fada mashi tana kuka cewa yayi gashi an zuwa domin shima hankali yayi mummunan tashi dajin wannan lbr hmm 🥺

30minutes later sai ga daddyn marwan ya shigo da mota haka ya gansu jigun jigun ga hidaya can gefe rana ya kare mata fuskantar duk jini kuma babu wanda yake kusa da ita..

Tana ganin mijin ta tashi da sauri ta na fadin " Daddyn marwa kaga abunda ke faruwa ko daddyn marwan meyasa mutane suke hakane meyasa zasu cuci baiwar Allah ma tayi masu" ? Nan yake ce mata tayi shiru ta kyale ina Abba Jadwa sai ta tunana mashi part in umma tace tun faruwar abun bai fito ai na fada maka yadda muka yi dashi, ya daga kai yace toh bari naje ko zai fito sai ya mike ya bi sai part in umma ya fara knocking.

Abba ya fito lokacin ya shirya tsaf zai fita sai suka gaisa nan daddyn marwan ya fara nuna ma Abba rashin dacewar abunda yayi
Aiko Abba ya ci ma daddyn marwan mutumci kamar ba shi ba yace shi sam bai san da wannan zance ba kuma su fita mashi gida baya son ganin su.
Cikin mamaki daddyn marwan ke kallon Abba abun ya daure mashi kai sosai. Yace toh ya mashi izini yana so su tafi da hidaya domin su nema mata gani baza'a barta a haka bah. Kai kawai ya daga alamun ya amince amma bai yi magana ba ya wuce shi yaje garage ya dauki motar shi ya fita ko kallon idan hidaya take baiyi bah.

JADWA (Completed)Donde viven las historias. Descúbrelo ahora