JADWA 27

56 4 0
                                    

Gama sujood inta tana murna tana gode ma Allah har suna jin ta cikin waya koda ta gama tana mommy mommy mommy said taji shiru sistern mommyn ta ta karbi wayan ta fara magana tace kinsan jikin sai a hankali yanzu amma tabbas mommyn ki ta ji sauki sosai ba kamar da ba yanzu ta fara magana kadan kadan kuma tana sallah tana cin abinci haka muke bata magani kullum kuma addu'an ki da kike yi ne jadwa ki ci gaba da addu'a kinji In'sha'Allah ko Abban ki zaki fara ganin chanji baza'a tabbata a haka ba taji dadi sosai harda kuka tana godiya suka ce zasu taya ta murna idan sun samu lokaci idan kuma basu samu lokaci ba toh zasu turo mata da kudi tayi hidimar graduation.

Tayi farin ciki sosai suka yi sallama.
Nan take ta kira zainab ta fara bata labari, tayi murna ita ma kamar zata fito cikin waya kan murna tace mata bari ta kira su taji, ai ko haka tayi sunji dadin yadda zainab ke son hidaya kuma take kula da Jadwa sun fada mata cewa tabbas hidaya na samun sauki kuma ba kamar yadda suka dawo da ita ba kuma tana magana yanzu kadan kadan.

Anyi graduation an gama zainab da daddyn marwan sun zo bauchi amma yan uwan hidaya basu samu zuwa ba sun dai tura mata da kudi kamar yadda suka ce zasu yi mata kuma taji dadi.

Ita ko umma an zama oga cikin gida yanzu ma shirye shiryen zuwa Saudi ake yi domin ta iya mota haka A'isha ta koya ita ma.

Bayan wucer umma saudi hankali Abba ya fara dawowa kan yar shi jadwa amma har yanzu fa baya son maganar hidaya, idan sun zauna suna fira da jadwa da Abba tana mashi maganar mommyn ta amma sai ya kama kaucewa baya so amma yanzu suna fira sosai da jadwa.

Su A'isha sun gama secondary school suma radiya ce kawai ke Ss3 sun ce ma umma sai lallai basu yi schl a Nigeria ba su sai dai ake su Malaysia ko China amma sam basu zauna Nigeria ba.
Umma ta goyi bayan haka tace tabbas idan ta dawo hakan zagaye dole Abba ya biya masu kudi su je waje karatu.

***
Abba ne yau ya shigo parlour umma, jadwa tana kwance tana kallo tashi tayi ta gaishe shi "ina yini Abba"? Yace lafiya lau jadwa ya kike ya gida lafiya lau ta fadi kai tsaye sai ya zauna yace jadwa ina so na tambaye yi ina kike sha'awar zuwa yin karatu ? Sai tace Abba Ni duk inda ka kai Ni yace ra'ayin nake son ji yanzu tace toh Abba yanzu ka barni nan Bauchi sai nayi karatu na anan kullum naje na dawo. Yace kin tabbata kinfi son haka? Tace eh na fi son haka. Yace toh shikenan zan sama maki admission ance zan ji ra'ayin yan uwan ki suma idan Allah yasa ra'ayin ku ya zo daya sai ku tsaya nan ku cigaba da karatun zai fi tace toh Abba ta fadi na kallon shi cikin ido tana so tayi mashi maganar mommyn ta sai ta kyaleni shi dai shima yayi mamaki da irin kallon da take yi mashi, Sai ya mata sallama ya bar parlour.

Da safe jadwa ta je part in Abba ta gaishe shi da safiya yace taje ta kira mashi A'ishah da Fatima taje ta kira su koda suka je yayi masu fada sosai akan rashin zuwa gaishe shi da basu son yi sai ranar da suka ga dama yayi masu magana akan makarantar school duka suka hada baki suka ce su Malaysia suke son karatu ko china.. kallon su ya tsaya yi yace meyasa baza suyi anan cikin garin bauchi sai suka suka bata rai suka ce su sunfi son can yace toh shi kam ba zai iya fitar dasu waje ba inda ma ace maza ne toh zai iya kai su amma gaskiya tunda matane su suyi hakuri su tsaya gida suyi karatun su idan su gama suyi aure.. ya na gama fadi ya tashi ya wuce toilet, wuce wa suka yi suna mugun magana idan umman su na gari ya da bai fada masu haka ba ai zata ta dawo kuma zata ji su idan ba su fita waje karatu ba sai dai su zauna gida ba karatu suka yanke shawarar hakan.

Bayan sun koma dakin su suke fitar tsakanin su A'isha tace"yanzu ita ma wannan munafukar yana nufin harda ita nan zai tsaya da ita? Sai Fatima tace waya sani yanzu ai sai umma ta dawo za muji komai duk da distinctions in da ta samu a result inta shine zai tsaya da ita Nigeria? Nigeria ma a Bauchi tabb lallai aiko akwai aiki don ni dai idan bauchi zan shiga karatu na yafe wlh.

Suna gama wannan Suratun suka kira umma suka fada mata tace ai bai isa bari dai ta dawo ya ga tsawon ta.

Da safen ya asabar umma jirgin su ya sauka su Hajiya umma manya Abba ne yaje dauko ta da ganshi, suna sauka yace hajjaju mutan Makka da madina umma ta wangale baki tace Alhaji na na kaina sai suka yi dariya duka mutanen da ke wurin ma burge su sukayi haka aka gama sa mata kayan ta cikin booth sai gida..

JADWA (Completed)Where stories live. Discover now