66-70

680 65 0
                                    

Maryam S Indabawa😍😘: *NAJWA*

BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻

DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH*


PAGE *66-70*


Yana gama shirin sa yayi dakin Mami. Lokacin ita ma ta shirya cikin wata atamfar ta fara da ja.

Farin mayafi ta yafa da jaka da takalmi tayi kyau da ita.

Sun fito ya bude mata gidan gaba.
Suka dau hanya.


*-*-*-*-*-*

"Assalamu Alaikum!"
Wata murya me dadi da sanyi tayi sallama a cikin wani katon gida.

Me gadin gidan dake gefe, ya washe baki, ya amsa masu da
"Wa'ailaikum salam!"

Suma fara'a dake kan fuskar su ta fadada. Suka zube a kasa. Suna gaishe shi.
"Baba ina yini?"

"Lafiya lou Basma da *Najwah* kun dawo lafiya."
Ya amsa musu cikin sakin fuska.

Suma cikin fara'a suka amsa masa.
"Lafiya lou."
"Masha Allah!"
Suka mike suka shige ciki.

Da sallama suka shiga katon falon nasu, wanda ya Wadatu da kayan alatu, kujeru ne a jere a dakin gefe kuma kayan kallo.

Sai can gefe kuma wajen cin abinci ne, sai matattakala da zata sada ka da saman gida.

Mahaifiyar su suka hanga akan sallaya da carbi a hannu tana jan sa.

Da gudu Basma tayi gun Maman tasu ta haye cinyar ta.

Basma ta ce,
"Mami nah Ya gida."

Mami ta amsa tana shafa kan ta.
"Lafiya lou Basma."

*Najwa* ce ta karaso dakin, itama a jikin Mami ta zube,
"Mami sannu da gida."

"Yauwah!"
"Ya gidan?"

Mami ta ce,
"Lafiya alhamdulilah."
"Masha Allah!"

Ta mike tayi sama, tana cewa,
"Basma taso a cire kayan makarantar ko?"

Basma ta amsa da
"Toh! Adda."
Ta mike ta bi bayan ta.

A saman ma wani falo ne shima wanda aka saka masa Kujeru da kayan kallo.

Wani daki ta bude, daki ne me kyau a kasa masa gado madai dai ci, da katuwar durowa, sai labulaye.

Basma ta fara cire wa kayan jikin ta, ta dauki wadan da suka cire dazu ta saka mata.

Riga da wando ne, irin Pakistan din nan. Ruwan hodar riga da ruwan gayen wando.

"Jekiyi alwala magariba tayi,"
"Toh Adda."

Ta shige ban dakin dake dakin tayo alwala, ta fito tayi Can falo.

Kayan jikin ta *Najwa* ta cire, ta sa irin kayan da ta sakawa Kanwar ta Basma.

Alwala tayo, ta fito ta hau kan sallaya tana tasbihi, har akayi kiran sallah magariba sannan ta mike ta tada sallah.

Sai da tayi isha'i sannan ta yo shafa'i da wuturi sannan tayo Falon gidan nasu.

Mami ta hanga ita da Basma na zaune.

Gefen su taje ta zauna, ta ce,
"Mami su Hamma da Dady basu dawo ba."

"Eh basu shigo ba amman nasan yanzu dau suna hanya."
"Toh Allah dawo dasi lafiya."

Mami ta amsa da,
"Ameen. Ya makarantar?"

"Lafiya Mami."
"To Allah bada sa'a."

"Ameen."

Mami ta kalli Basma ta ce,
"Basma ana dai gane karatun ko?"

Basma ta ce,
"Eh Mami."

"Masha Allah. Allah kara basira."
*Najwa* da Basma suka amsa, da
"Ameen."

Dai dai lokacin su Dady da Hamma Salim sukayo sallama.

Da gudu Basma tayi gun Dady ta rumgume shi tana, ce wa.
"Dady oyoyo!"

Shima rumgume ta yayi,
"Oyoyo Basma ta."

Ya karaso cikin dakin. *Najwa* ta kalli yayan ta. Ta ce,
"Hamma Salim sannu da zuwa ya hanya."

"Lafiya lou *Najwa.* "
"Masha Allah."

Ta juya gun Dady, ta ce,
"Dady sannu da zuwa."

Dady ya, amsa mata, da
"Yauwah!"

"Ya hanya, ya aiki?"
"Lafiya Alhamdulillah!"

"Dady Allah kada budi."
"Ameen *Najwa* "

Mami ce ta masa sannu da zuwa sannan suka mike sukayi sama.

Ya Salim ma sama ya yi dan rage kayan jikin sa.

*Najwa* ce ta kalli Basma, ta ce,
"Yauwah Basma, biyo min haddar da zaku bayar gobe."

"Toh Adda! Suratul Mulki ce."
Nan ta fara rairowa ta tare da fitar da ko wanne hukunci.

Karatun nata me dadin sauraro da fitar da ko wacce harafi,

Sai da ta gama sannan tace ta karanto mata tauhidin da tayi musu yau aji.

"Basma, karanto min Tauhid din da na karanta muku a aji."

"Toh Adda."
Ta dauki littafin ta, ta fara karanto mata.
"Su sa'al:-Man kala kalaaka?
Tambaya:-Wanene ya halice ka.

Ja jawabi.:-Allahu huwa lazi kalaqani, wa kalaqa kulli shai'in
Amsa:-Allah shine ya halice da dukan komai."

"Masha Allah! Da kyau."

Mami ce ta sauko, ta ce,
"ah lalai Autata kina kokari kema."

"Mami so nake nima na zama kamar Adda."
"To indai kina so sai kin dage kinga itama ba. A zaune take ba."

Mami ta kalli *Najwa* ta ce,
"Toh *Najwa* Menene tsarki gaba daya. Da bayani akan sa."

*Najwa* ta ce,
"Mami a cikin wani littafin Fikihul miyasir. Malamin yace,
Abubawa biyu ne ke sa ayi tsarki da karamin hadasi sune
tusa, fitsari, maziyi, da wadihi. Wadan nan alwala suke wajab tawa
Janaba, nifasi, haida, sune babban hadasi su wanka suke wajab tawa.

Sharadi ne ayi tsarki dan ingantuwar sallah.
Tsarki, :- shi tsabta, dan kawar da dukkan datti da dauda.
Kawar da najasa daga jiki, da wanka, dan kawar da bababn hadasi, haka ma alwala tsarki ce kamar yadda taimama ma take tsarki."



*INDABAWA*

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now