125

583 59 0
                                    

*NAJWA*

🌐  *HAJOW*  🌐

*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻

By *MARYAM  S  INDABAWA*
*MANS*

DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH*

*ALLAH YA SAKA MIKI DA GIDAN ALJANNA.*
*AMEEN*

PAGE *125*

Zaunar da Najwa tayi zatai mata kwalliya.
"A'ah Sis yimin simple ban son me yawa."

Wannan yasa tai mata jagira kawai sai dan man lebe da ta shafa mata."

Ya salam duk da batai kwalliya ba. Amman ba karamin kyau tayi ba.

Waya aka kira Zahra, dauka tayi, ta ce,
"Gasu ban."

Mayafan suka yafa, suka fita. tin daga nesa ya zubawa Zahra ido.

Najwa kuwa tsaki tayi, ta ce,
"Wallahi Mustapha ya fiya kallo."

Hararar ta Zahra tayi ta ce,
"Dadin ta kayan sa yake kalla."

"Au haka kika ce?"
"A'ah amman ai dadin ta ma bamu san yadda naki zai ba in ya ganki."

"Ba ruwan sa ai."
"Allah Sis irin wadan nan sun fi fitina."

"Ke gidan su. Yayan naki ne fitanan ne."
"A'ah yi hakuri Adda."

"Allah sarki har kin tunon da Basma ta. ina kewar ta wallahi."

Mustapha daya karaso wajen shi ya katse musu maganar da suke yi.

Durkusawa yayi yana cewa,
"Adda ina yini?"

Hararar sa tayi ta ce,
"Dan Allah ku daina mai dani tsohuwa."

"Anki din!"
Zahra ta fada. Duka ta kaima tana dariya.

Gaisawa sukayi, sannan suka matsa gefe suka zauna.

Mota ce, ta danno wajen da suke, kallo suka bi motar da yi banda  Najwa da ke danna wayar ta.

Najib ne ya fito daga motar sanye da  wandon jeans,  sai jar riga idon sa sanye da tabarau me garai garai.

Ba karamin kyau yayi ba, sai tashin kamshi yake.

Zahra ce ta rage murya tana fadawa Mustapha wani abu.

Da sauri Mustapha ya mike ya taro shi suna gaisawa.

Karasowa sukai suka gaisa da Zahra, Najwa ta nuna masa da hannun ta.

Kallon ta ya tsaya yi, da ido baki da hanci. duk ya rasa control din sa dan ya saka daina kallon ta.

Dariya Zahra tayi, ta ce, a ranta.
"Nagodewa Allah naga yadda zatayi da shi. Shima ga kallon nan."

Hannun sa Mustapha ya kama ya kai shi gefen ta.

Kamshin turaren da taji shi yasa ta dagowa da sauri.

Ido ta zaro ta mikewa a razane, kallon sa take da alamun kamar ta sanshi.

Shima hakan kokarin tino inda yasan ta yake.

Kai ya girgiza, tini ai ya dade da sanin ta ko na ganin ta da yake.

Itama kawar da tunanin tayi, a ranta ta ce,
"Kama ce."

Kasa tayi da kai, kallo ya bita dashi.

"Ina yini?"
ta gaisar dashi murya na rawa.

Kallon ta yayi, dan son tino inda ga taba jin muryar nan.

"Lafiya lou Najwa ya karatu."
"Lafiya Alhamdulilah."

Shiru tayi. Kallon ta ya tsaya yi kamar TV.

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now