162

744 53 0
                                    

*NAJWA*

BY *Maryam S Indabawa*
*Mans*

Dedicated to *Rashida A Kardam*
*Anty Rash*

*Allah dafa miki. Allah karawa Mama lafiya da nisan kwana. Ameen*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya online writers*

*Allah kara mana hakuri da juriya.*
*Ameen*

*Gidan aminci da karamci. Allah kara basira Ameen*

Page
*162*

*Teemah*
*Tnc for ur prayer*
*I really appreciate*




Sai magariba suka koma gida dan har Mami sai da suka rakasu.

Bara'atu ta bar mata dan tana taya ta aiki.

Duk rashin lafiyar da Najwa keyi, be hana ta bawa Najib kulawa ba dan sai shi da yake hana ta.

Lallabawa tare da gatan ta ta kuwa sai abinda yai gaba.

Sosai take samun kulawa daga Mami zuwa ga Najib.

Kwado kuwa kullum sai an mata, haka nan Faten wake sai na Mami kawai take iya ci.

Bara'atu kuwa ba abinda bataiwa Najwa.

Sai da cikin Najwa ya isa wata daya sannan ta samu sauki take iya cin abinci ta daina aman nan.

Sumaiyya kuwa bata san halin da ake ciki ba.

Hamma Salim kuwa sai da yazo ya duba ta, mamin ta dai ta waya tai mata sannu.

Haka nan abokan Najib sai da suka zo, duk da Najwa bata da lafiya karba hannu bibiyu ta dinga musu.

Kowa yasan da cikin Najwa sai murna da Allah sanya alheri ake yiwa Najib.

Duk matan abokan Najib da suka zo sai sunce yanzu yai aure dan akwai fuska.

Khaleel da Khadija ma sunzo amman aranar suka juya.

Khadiya sai zolayar Najwa take.

Bangaren Najwa dai tinda aka gano tana da ciki bata rasa baki yan barka.

Kamar ko da yaushe yau Ranar kwanan Najwa ne wannan yasa tin safe take gyara bangaren nata dan tinda ta fara laulayi bata taba jin karfi jiki kamar yau ba.

Bangaren nan  nata sai da ta maidashi kamar sabo dan gyara.

Abinci kuwa ta daura masa danbun shinkafa wanda yaji kayan lambu sai farfesun kiji da tai masa.

Lemon kwakwa tai masa wanda yaji Madara yai sanyi.

Wanka taje tayi ta caba ado cikin wani Bakin three quartern wando wanda gwiwar sa net ne.

Wata farar riga ta saka wacce duk jikin ta net ne.

Kallon kanta ta tsaya yi a mudubi, cikin ta ta shafa wanda baza ka taba cewa akwai cikin wata biyu a gun ba.

Sai dai kirjin ta da ya ciko.
Kiran Sallah magariba taji anayi wannan yasa ta dauki wata doguwar riga ta saka.

Sai da ta idar da sallah sannan ta janyo wayar ta, Zahra ce ta kira.

Dagawa tayi ta ce,
"Yar uwa ya kike yau naji ki shiru?"

"Ina lafiya na kira naji ya lafiyar Babyn mu ne."
Dariya Najwa tayi ta ce,

"Yana lafiya. Ina Baby Fauwaz?"
"Kingan shi nan yayi bacci."

"Allah sarki a gaida min da Yaya Mustapha muna nan zuwa muma nan ba da dadewa ba."
Allah kai mu. Sukai sallama.

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now