86-90

672 56 0
                                    

*NAJWA*

By *Maryam S Indabawa*
*MANS*

*HAJOW*
*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


DEDICATED TO *ANTY RASH KARDAM*

Page *86-90*

Kayan Kwalliya Mamin Najib ta kaiwa Najwa da su turaruka masi tsada da kamshi.

Basma ce ta shiga dakin *Najwa* ta ce,
"Adda karatu kike yi."

"Eh Basma. yauwah Basma biyo min karashen karin ku na yau."
"Wanne Adda."

"Na tauhid."
"To Addah

"Su su'al:- Limaza kalakallahu?
Tambaya:- saboda me Allah ya halice ka.?

Ja jawabi:- Kalakani li'ibadatihi
Amsa:- Ya halice mu ne dan mu bauta masa."

"Masha Allah."
"Adda dan Allah ki kara min kafin ki mana kari."

"To
Su'al: Tambaya

Kaifa ta abudullaha? : tayaya kake bautawa ubanhijin ka?

jawab: amsa
A'abuduhu, kama amara,: ina bauta masa kamar yadda ya umarce mu.

Wakama amara rasulillhi
Kuma kamar yadda Manzon Allah ya umar ce mu.""

"Ina nabiya ki biya."
Haka suka dinga yi har sai da Basma ta iya.

Mami dake tsaye a bakin kofa tace,
"Toh *Najwa* Mecece Najasa?"

"Mami a cikin fikihul miyasar, malamin yana cewa,

"Najasa:- Fitsarin mutum, da bayan gidan sa, da wadihi, da maziyu, da jinin haila, da na nifasi, da yawun kare, da fitsarin abinda aka haramta cin sa, da kashin sa, da matattaun dabobi na kan kasa, me jini. sune najasa.

Sannan Fitsari bayan gida, waziyi da wadihi, sune abubuwan da in kayi su ko ka same su sai ka sake alwala. Su ake kira da karamin hadasi.

Janaba, da haida, nifasi kuma sune wadan da in ka same su sai kayi wankan tsarki. Su ake kira da babban hadasi."

"Menene janaba?"
Mami ta tambaye ta, bayan ta gama jawabin.

"Mami Janaba:- wata abace nau'i biyu.
1- fitar mani dan wata sha'awa da ta samu mutun a cikin bacci ko ido biyu. Shine janaba

2- ko kuma haduwar fatu guda biyu (haduwar farjin mace da na miji) idan an samu haka ko mutun be fitar da komai ba wanka ya wajaba a gareshi wannan ita ce janaba."

" *Najwa* da akwai, banbancin tsakanin fitsarin yaro karami da babba?"

"Eh! Da akwai, fitsarin yaro karami yayafi ya isar masa.  Sabanin na babba (Malam me fikihu ne yafada.) Wannan yana nufin fitsarin yar karami in aka yayafa ruwa ya isa. Na babba kuma sai an wanke."

"Na mata fa?"
"Mami Malam me fikihu miyasir yana cewa, ita mace ko da takasan ce ana shayar da ita tayi fitsati sai an wanke shi.
Manzon Allah (SAW) Yace, " Fitsarin yaro karami yayyafi ya isar masa. Fitsarin yarinya karama a wanke shi."
Turmizi ne ya rawaito shi."

"Shin Mani najasa ce."
"A'ah Mami. Mani ba najasa bace. Dan akwai wani lokacin da Nana Aisha in ta samu mani a tufafin Manzon Allah (SWA)  Take kankare shi da farcen ta, kuma yasaka kayan yaje yayi sallah. wannan yana nuna kenan Mani ba najasa bane.

Sannan Nana Aisha tace, akwai lokacin kuma da zata sa ruwa dan kawar dashi, kuma ko be bushe ba, Ma'aiki (SWA) Yana sakawa yayi Sallah dasu.

Mami in har da Najasa ce, sai Manzon Allah ya tabbatar da an wanke su.

Akwai hadisin da Manzon Allah (SWA). An karbo daga Jabir dan Samrata. Yace,
"Wani mutun ya tambayi Manzon Allah (SWA) shin zan iya sallah da tufafin da najewa iyali na.
Sai Manzon Allah (SWA) yace,
"Eh sai dai in yaga wani abu a jikin sa. Sai ya wanke." Ibn maja ne ya rawaito shi.

Fadin malamai da yawa wasu sunce mani ba najasa bace, wasu kuma sunce najasa ce. Allah shine mafiyin sanin gaskiya."

Salim ne ya karaso dakin. Yace,
"Mami wallahi kun bar mu da yunwah."

"Ayyah kuyi hakuri ban san kun sauka kasa bane. Gamu nan."

Salim ya ce,
"Mami ai sai nasa ku a gaba. In ba haka ba nasa baza ku taso ba."

Murmushi *Najwa* tayi, ta ce,
"Mami tashi muje an bar Dady da yunwah."

Ta fada tana kama hannun Mamin tata. Mikewa tayi suka sauka kasa dan cin abinci.



*-*-*-*-*-*-*-*
Karfe goman dare.

Cikin sanda take shiga cikin gidan nasu. Muryar Mama taji tana cewa.
"Zo nan."

A firgice ta juya tayi wajen Maman tata. Mama ta ce,
"Sumaiyya wai me kike yi haka ne, yanzu karfe nawa?"

Shiru Sumaiyya tayi. Mama ta cigaba da magana
"Ace kina mace ki kai karfe goman dare a waje wannan ai ba mutunvin ki bane. Ba wani dalili sai na yawo da har zaki kai karfe goman dre a waje."

Sumaiyya baki da turo gaba ta ce,
"Mama kiyi hakuri."

Mama ta girgiza kai, ta ce,
"Sumaiyya ki canja hali ki sani ke mace ce, yan da kyu kina yin tsafta da sanin abinda kike. Amman ke kullim yawo shine a gaban ki dn kinga Abban ku na kyale ki ko. Tashi ki bani waje."
Daki tayi tana mita.

Dakin ta Sumaiyya ta shiga, kaca kaca da shi, daga ledar biskit sai ta alawa, sai kwalon lemo.

A haka ba tare da ta kawar da komai ba, ta hau kan gadon da ba gyara ba komai ta kwanta.

Tunanin irin shigar da zatayi a bikin da zasu yi take dan tasan Bashir babban mutum ne ko zata samu itama mijin aure.

Sumaiyya bata da buri sai na tayi samari wadan da zasu na kashe mata kudi. Samarin ta yawa ne dasu haka nan kuma, kowa tatsar sa take, amman ba duk da haka bata barin ayi wani abu da ita.

Sai dai shigar banza, da son kudi. Sumaiyya ba abinda ta iya. Dan ko gyaran daki ma bata iya ba bare yin girki.

Kan ta sai yayi wata a kitse bata tsefe ba, ko zata tsefe sai dai taje saloon a tsefe a wanka mata wani lokacin sai yayi wata zata wanke.

Kaya kuwa duk da tana da masu wanki amman kafin ta dauka ta bayar a wanke aiki ne a wajen ta.

Sai dai tai tayin sabon dinki. wannan halin sumaiyyan na damun ta maman ta.

Duk yadda taso tasata a hanya abin yafi karfin ta. wannan yasa ta hana masu musu aiki gyara mata daki a ganin ta zata na gyara wa amman ina ba ruwan ta haka take rayuwa a dakin duk datti da kura.

Addu'a kuwa Mama bata fasa ba na kan Allah ya shirya mata yarinyar ta.

Ga wani girman kai da Allah ya daura mata. Dan ko ya'yan yan uwan Mama duk bata son su ko magana bata hadasu. Ko dan Allah ya rufa musu aisri ne ko mene ne oho.

Duk fadan da Mama zatayi sai tace ai ba sa'anin ta bane yaran da ta basu shekara wajen bakwai tayaya zatayi mu'amala dasu.



*INDABAWA*

NAJWA Complete ✔Tahanan ng mga kuwento. Tumuklas ngayon