115

553 54 1
                                    

*NAJWA*

🌐 *HAJOW* 🌐

*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻

By *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*

DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH*

*ALLAH YA SAKA MIKI DA GIDAN ALJANNA.*
*AMEEN*

PAGE. *115*

Najib kuwa wayar sa ma a gida ya manta ta bare har ya kira Summy, Number Momy kawai ya rike sai ta Khaleel.

To amman bazai kira Khaleel yanzu ba dan yasan zai kawo masa maganar Summy shi kuma baya so.

Yana sauka ya turawa Mami ya sauka lafiya yanzu haka yana ta harka akan abinda yaje yi.

Fatan Alkhairi Mami ta kuma yi masa tare da kara fada masa yaji tsoron Allah.

Summy kam kullum Khaleel zai kira haka nan zai turo mata da kati. Amman ita tafi son taga Najib ya kira ta

Duk harkar shirmen ta, ta daina, sai dai halin ta na son jiki da rashin son gyara da har yanzu yake nan.

Samari kuwa duk ta watsar dasu. Yanzu kawai jiran kiran Najib take da dawo war sa ayi abinda za'ayi.


Dady da kansa ya kai Najwa Har Abuja lokacin Dadyn Najib ya dawo bai kwana ba a ranar ya juya da yake tafiyar jirgi ce.

Su Mami kuwa ba karamin murnar zuwan ta sukai ba, Mami sai nan nan take da ita.

Daki dake kusa v
danata ta kai ta, sannan ta kai mata abinci da kanta.

Wanka tasa tayo sannan ta kwanta dan ta huta.

Kwanciya kawai tayi dan ta kasa baccin ma.

Zaman da Najwa tayi a Abuja sosai ta huta dan sam ba abinda take yi.

Kullun Mami ta dauke ta, ta kai ya yawo ko shopping ahaka tayi har tayi sati biyu sanna ta fara shirin komawa.

Kullum sai sunyi waya da Najib, lokacin da tafiyar ta tazo sosai Mami ta hada mata kaya banda na kwalliya ga sutura.

Dady da Mami da kan su suka kai ta kano. a gida kuwa sai kewar ta ake yi bama Basma.

Dawowar ta da sati biyu ta daga katsina, gidan Anty Hauwa kanwar Mamin ta.

A can ma sai murna zuwan ta ake bama Zahra. Daki daya aka bata wanda aka zuba mata komai a ciki.

Komai an gama musu dan karatu kawai suka fara. Kullum a kai su a dauko su.

A haka har suka yi rabi a semister karatun su. Kullum sai sunyi waya da gida da Hamma Salim.

Sai da lokacin Jarabawa yazo sannan suka koma hostel da zama. A hostel din ma Kullum sai momy ta aika musu da abinci.

A haka har suka kammala first semestern su. A katsina tayi zaman ta. Dan Mami ta ce kada tana yawan zirga zirga akan titi.

Duk wata sai Mami ta aiko musu da dinki da fashion ta ce ana zuwa makaranta dasu. Haka duk wata Abban mahaifin Zahra sai ya basu kudi sun shiga kaswani da store kowa yayi siyayyar abinda yake so.

Haka nan Dadyn Najwa shima duk wata zai turawa Zahar da Najwa kudi a account din su.

Najwa najin dadin zaman ta a katsina kowa son ta yake.

Najib sai da yayi wata biyu be kira abokin sa ba shima duk dan kada ya kawo masa maganar Sumaiyya ne.

Ganin bazai iya jure rashin kiran abokin nasa va yasa, ya dauki waya ya kira shi.

Gaisawa sukayi kamar ba komai, Najib ne ya ce,
"Bro daman number Summy nake son ka turo min."

Wata dariyar rainin hankali Khaleel yayi, ya ce,
"Wacce haka?"

"Dan Allah kayi hakuri wallahi abubjwa ne sukai min yawa kuma na manto wayata a gida shi yasa ko Mami da kyar na tuno number ta yanzu haka ma ita ta turon taka."

Murmushi me sauti Khaleel yayi ya ce.
"Ka daina karya ba halin ka bane. ba komai zan turo maka ita yanzu kasan yadda zaka ce mata "

"A'ah dan Allah kada kayi min haka. Ka dan tsara ta yadda zata yadda da abinda zan ce mata."
"Oho maka ni ba ruwana."
Ya katse kiran.

Number ya tura masa yana dariya. Yana tura masa ya kashe wayar gaba daya dan yasan in ba haka yayi ba bazai barshi ba. Sai ya dame shi da ya kira Sumaiyyan shima.

Nan kuwa besan ya riga ya fada mata ceewa Najib ya manta wayar sa shiyasa ko gida be nema va. Amman da ya kira gida yasan zai neme shi ya bashi number ta.

Wanann yasa sam hankalin ta be tashi ba akan rashin kiran da be mata ba.

Amman kwana biyun nan Maman ta, ta matsa kan ta fito da miji abinda ya fara damun ta kenan.

Gashi yanzu ba wanda take kulawa duk ta zubar da samarin ta ganin ta samu Najib.

Kwance take tana tunanin sa, taji karar wayar ta. Dauka tayi jiki a sanyaye.

Sabuwar number ta gani kuma bata kasar ba. Bata kawo shine ba dan haka ta kara a kunne ta. Tare da cewa
"Hello."

Tsaki yayi a cikin ransa dan shi ya tsani wannan dabi'ar ta hello kafin kayi sallama.

Sallama yayi mata cikin muryar sa me dadi.

Mikewa taayi daga kwancen da take da sauri. Dan sau dayan da taji muryar sa ko ina ne baza ta taba mantawa da muryar ba.

Muryar da ita kadai ma gizo take mata. Nutsuwar ta, ta dai dai ta, ta amsa masa da
"Wa'alaikum salam "

Shiru sukayi gaba dayan su. Ita ce tayi karfin fara magana da gaishe shi.

Amsa mata yayi, rasa abin fadi yayi. Da kyar ya daure ya ce,
"Kinji ni shiru ko?"

"Lah ba komai ai, Khaleel ya fada min ka manta wayar ka ne. Ya kake ya aikin?"

"Lafiya lou Alhamdulilah "
"Masha Allah daman kira nayi mu gaisa zan kira anjima."

Ya katse wayar. Wayar yabi da kallo yana mamakin wai shine yake magana da wata a nufin saurayin ta

To ya zaiyi auren shine kadai samun saukin sa. Dole yayi tinda Allah yasa be ga wacce yake so din ba.

Summy kuwa dadi kashe ta murnar da take ciki sam baza ta musaltu ba.

Ta rasa wane irin farin ciki zatayi da ya kirata.


Cikin ikon Allah har su Najwah sun shiga level two karatun su Alhamdulilah basu da matsalar komai dan karatun suke sosai.

Kuma result din su me kyau ne. Tin zuwan Najwa katsina bata taba zuwa gida ba.

Amman wannan karan Momy ta ce zasu tafi ita da Zahrah.

Murna gun Najwa bazata misalti ba dan tana son zuwa gida

Lokacin da Hamma Salim yayi graduation duk yan gida sunje amman ita karatu ya hana ta zuwam.

Hamma Salim da kansa yaje har katsina yayi mata kwana ki sannan ya koma gida ba karamin jin dadin zuwan sa tayi ba.

Ko a makaranta su Najwa abin sha'awa ne sam basu da kawaye sai dai classmate da suke yin zumunci a karatu.

Saurayi kuwa sam basa kulawa bama Najwa da an mata magana zata ce tana da mijin.

Gara ita Zahra tana da wanda zata aura ma dan gidan abokin baban ta ne

*INDABAWA*

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now