76-80

659 63 0
                                    

*NAJWA*

BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*

*HAJOW*
*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻

Page*76-80*

Dedicated to *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH*


Sai karfe sha biyun rana, sannan *Najwa*  ta sauko,  kitchen ta shiga kai tsaye, ta daura abincin rana.

Shinkafa ta dafa wacce taji kayan lambu, sai miya da tayi ta saka mata naman kasuwa. Sai peppe chicken da tayi musu.

Sai hadin salad, da lemon ginger wanda ta saka masa zallar ginger da lemon tsami sai suga. ta saka a firij.

Duk yadda Mami taso ta tayata amman sam *Najwa* taki yadda.

Dan haka sai kallo take binta dashi tana aikin ta

Tana son yar ta. Dan tana da ladabi biyayya ga ilimi, ga amdani dashi dan komai nata cikin nutsuwa da ilini take yin sa

Tana gamawa ta wanke wanje sanna ta jere kanukan a wajen da suke cin abinci.

Karfe daya da rabi ta shige ban daki dan yin wanka. Tana fitowa har Basma ta dawo.

"Adda ina yini ya gida?"
Murmushi *Najwa* tayi, sannan ta amsa mata da.

"Lafiya lou Basma. Ya makaranta?"
"Adda makaranta tayi ddi yau an mana test naci maki me yawa."
Murmushi *Najwa* ta karayi

"Masha Allah haka nake son kanwata"
Basma tayi murmushi.

"Nima so nake na zama kamar Adda ta, saboda na zama me ilimi da amfani dashi."

Murmushi *Najwa* tayi ta kamata, ta cire mata kayan makaranta, sannan suka shige ban daki tayi mata wanka.

Suna fitowa, *Najwa* ta shirya kanwar tata, cikin kayan makarantar ta.

Wanda suke a wanke a goge,  ta feshe ta da turaren ta.

"Basma maza je kici abinci kafin na sauko."
"Toh Adda!"

Tana fita itama ta shirta cikin kayan makarantar ta, ruwan omon riga da wando da ruwan daurawar hijabi wanda ya wuce gwiwar ta.

Bata fesa turare ba, sai humra da Ambar da ta cakude jikin ta dasu

Nan take ta fara fitar da kamshi me dadi, fuskar ta duk da batai kwalliya amman tayi kyau.

Jakar ta, ta dauka da ta Basma, sannan ta bude loka ta dauki Nikaf.

Kasa ta sauka lokacin har Basma ta gama cin abinci.

"Mami zamu tafi."
"Bafa kici abinci ba."

"Mami na koshi sai mun dawo."
"Toh shikenan."

Mami ta fada tana bin bayan su,

Najib da Mami ne, acikin mota suna tafe suna hira bin sha'awa.  Har suka shigo cikin titin sabuwar kofa.

Wani sanyi yaji ya ratsa shi, ganin sun shigo unguwar da ya hadu da yarinyar da ta burge shi.

Katon gida suka nufa, horn yayi me gadi ya bude masa, bayan sun gaisa.

Fitowa Yayi, ya budewa Mami, sannan yace,

"Mami shiga gani nan."
"Ina zakaje?"

Kai ya sosa, yana murmushi. Itama Murmushi Mami tayi,

"Son yarinyar zaka nema ne."
"Eh! Mami dan naga yan makarantar na wucewa."

"Kar dai, ka tsayar da ita a hanya."
"Mami na bazan yi haka ba."

"Jeka sai ka dawo."
"To Mami."

Ya shige motar tasa, ya fita ya koma ta inda ya ganta ranan.

Suna tafe Mami da su *Najwa* , *Najwa* na saka nikaf a fuskar ta.

"Yau kuma *Najwa* "
Mami ta fada tana kallon ta.

*Najwa* ta ce,
"Wallahi Mami, ido yana min yawa a wajene shiyasa."

Murmushi, Mami tayi, suna shan kwana suka hadu da Mamin Najib. Na karasowa.

Murmushi ne ya sauka a fuskonkin su. Basma kuma tayi wajen Mamin Najib da gudu tana

"Oyoyo Mami nah."

Mamin Najib ta ce,
"Oyoyo Basma, za'a tafi makaranta ne."

"Eh! Ina Ya Najib?"
"Ya Najib ya fita yanzu zai dawo."

Mami ta karaso gun su *Najwa* rike da hannun Basma.

Har kasa *Najwa* ta durkusa tana gaishe da Mami ta amsa, cikin sakin fuska.

Mamin Najib ta ce,
" *Najwa* yan mata, za'a tafi makarnta ne?"

*Najwa* kanta a kasa ta ce,
"Eh Mami, yasu Hamma Najib, da su Dady."

"Suna lafiya. Tare muke da Hamman naku ai."

"Mami mu shiga daga ciki ko?"
"Toh! Najwa, ku tafi Allah kiyaye hanya."

SuKa hada baki suka ce,
"Ameen! Mami. Sai mun dawo."

Mamin Najin ta ce,
"A dawo lafiya."

Suka fice, duk da ta titi yafi saurin zuwa makarantar amman *Najwa* ta jasu suka bi ta bayan layi.

Ya jima zaune a cikin motar sa, yana jiran ganin wucewar su, sai da yaga baya ganin kowa sannan ya juya jan motar ya koma gidan su *Najwa* jikin sa duk a sanyaye.

Lokacin su Mami na daki ana ta hirar yaushe gamo.

Su Dady ba shiga, shima Najib ya shiga da motar sa.

Kallon suka bisa dashi, dan basu gane wanda ya shigi ba. Sai da ya fito sannan suka gane shi.

Salim ne yayi wajen sa, yana zuwa ya rumgume shi. yana cewa,
"Hamma Najib ka yadani."

Najib ya bubugi bayan sa, ya ce,
"Tayaya zan yada dan uwana."
Ya fada yana rumgume shi.

Sakinsa yayi, yayi wajen Dady, ya duka har kasa, yana gaishe da Dady, da sauri Dady ya dago shi yana mika masa hannu. Ya ce,

" 'Dana, ya kuke?"

Najib ya amsa, da
"Lafiya lou Dady!"

"Ya Mamin taka?"
"Mami tare muke tana ciki. Dady kun dawo lafiya?"

"Lafiya lou  mushiga daga ciki."

Suka yi cikin gidan hannun Najib rike da Hannun Salim.

Suna shiga Mamin *Najwa* ta mike ta kamo hannun sa. Ta ce,
" 'Dana, yau kaine a gidan namu."

Murmushi yayi ya dukar da kasan kasa. Ya ce,
"Mami ina yini?"

Mami ta amsa,
"Lafiya lou 'dana. Ya kuke ya aiki?"

"Mami komai lafiya."
"Masha Allah,"

"yasu *Najwa* da Basma."
"Sun tafi makaranta."

"Wai na jima ban gan Autar daru ba."
"Ai auta yanzu anzama yan mata."

" *Najwa* fa?"

"Baka manta da yar gidan naka ba."
Salim ya fada cikin zolaya.

Najib ya ce,
"Ina Salim! Tayaya zan manta da *Najwa* ta."

Murmushi sukayi gaba daya. Mami ta ce,
"Ku tashi muje kuci abinci."

Suka mike, sukayi wajen cin abinci, Dady da Mamin Najib na hira.

Suna gamawa, Dady yace, su taso suje gidan su Ummah, daga nan kuma suka tafi gidan Ammi,  mama Amina.



*INDABAWA*

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now