147

632 44 0
                                    

*NAJWA*

BY *Maryam S Indabawa*
*Mans*

Dedicated to *Rashida A Kardam*
*Anty Rash*

*Allah dafa miki. Allah karawa Mama lafiya da nisan kwana. Ameen*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya online writers*

*Allah kara mana hakuri da juriya.*
*Ameen*

*Gidan aminci da karamci. Allah kara basira Ameen*

Page *147*

Na gaida ke, *Princess Amrah* Ina yinki. Allah kara basira da zakin hannu. Allah saka miki da alheri.
*Ameen*



Summy kuwa bata tashi dawowa ba sai karfe dayan dare, lokacin Najib har yayi bacci.

Ganin fitilar barandar sa a kunne wannan ya tsorata ta. Amman ta dake tayi cikin dakin ta.

Kwanciyya tayi tana sake sake a ranta taje ko kar taje  daga baya zuciyar ta, ta yanke mata hukunci akan tayi kwanciyyar ta. Ai kuwa haka akayi.

Washe gari da safe ta tashi da wuri ta shiga kitchen ta saka masu aiki su shirya mata break dan akwai abinda boka ya bata ta saka masa a abinci.

Dankali tasa aka soya masa sai ruwan tea da farfesun kayan ciki.

Bangaren sa ta kai masa wanda shi ko tashi beyi bama.

Dakin ta, ta koma ta zauna tana jiran fitowar sa.

Sai karfe sha biyu ya tashi yana tashi yayi wanka ya shirya cikin wani farin yadi.

Wayar sa ya dauka ba abinda ya gani sai sakon Najwa.

Murmushi yayi ya kira ta.
"Barka da safiya ranka ya dade."

"Barka kadai  baby na. Kin tashi lpy."
"Lafiya lou Alhamdulilah. Ya ka tashi?"

"Na tashi lafiya Amarya ta. Yasu Mami."
"Lafiya suke."

"Masha Allah daman zan fita nace zan kira, zanje wajen Mami, daga nan zan leka asibiti."

"To Yallabai! Allah ya dawo dakai lafiya Allah tsare min kai. Ka kular mana da kan ka."
"Kedawa?"

"Antyna man."
"To sai anjima."

Sukai sallama shi sai a lokacin ma ya tina da Sumaiyya.

Fita yayi, har zai fice daga gidan ya dawo dan duba ta.

Tana zaune a falo ba laifi tayi kyau da ita.

Tana ganin shi ta mike, kallon ta yayi ya dan yi murmushi.

Zama yayi, ya ce,
"Ina kika je jiya."

Kame kame ta fara yi. Kallon ta yayi yaga ba alamun gaskiya a tare da ita.

"Kiji tsoron Allah dai ki sani duk abinda kike Allah na ganin ki. Kuma Allah zai tambaye ki. hakanan duk abinda kike kina tsoron Allah kuma ki sani in ni da wanda kika je gareshi baya ganin ki Allah na ganin Kuma zai nuna aranar Alkiyama ranar da babu yafiya komai yazo karshe. Kiji tsoron Allah ki sani raba 'da da mahaifi ba abune me wahala ba. Amman in har Allah ya baki nasara to ki sani Allah ya jarabbce ki da babban laifi kina addu'a Allah ya yafe miki. Ni dai mijin kine kuma bazan so wani abu maea kyau ya same ki ba. Ki sani abinda kikai min na yafe miki."

Mikewa yayi ya nufi hanyar fita. Baki ta tabe ta bi bayan sa.

"Kayi hakuri."
ta fada dai dai lokacin da zai shiga mota.

"Naji."
"Kaci abinci to?"

"No i am fasting."
"Sai ka dawo "

Ta fada tana shigewa ciki.

NAJWA Complete ✔Tahanan ng mga kuwento. Tumuklas ngayon