91-95

647 57 0
                                    

*NAJWA*

BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*

*HAJOW*
*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


PAGE *91-95*

.DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH*


Yanzu abin har ya zaman masa jiki dan sai dai bai kwanta bacci ba amman mafarkan ta zai tayi. Yaga sunyi aure ko ya gansu a tare dai.

Najib ya rame saboda ba shi da kwanciyar hanakali. Burin sa kawai yagan ta kullum cikin bulayi yake amman sam bai kara gani ko me kama da ita bane.

Mami ma duk hankalin ta ya tashi dan gani yadda yaron nata ya koma, abin tausayi.

Yau Tin safe Khaleel ya je gidan su Najib dan ranar juma'a za ayi dinner abokin su, kuma ranar asabar daurin aure da kai amarya.

wannan yasa yazo dan yaji Najib din shiru kwana biyu.

A dakin Mami ya zauna, bayan zun gaisa yake tambayar ta Najib. Tace masa yana dakin sa.

Yayi mamakin yadda Najib baya  daki Mami kuma na dakin ta, dan ko da yaushe Najib na makale da Mami sai da kyar yake barin gefen ta.

Dakin ya shiga, yayi tsamamanin ma wanka yake shi yasa ya bar Mami ita kadai. amman sai ya ganshi a zaune, ya zubawa taga ido.

Salama yayi tafi sau uku amman Najib be san ana yi ba. Cikin dakin Khaleel ya shiga.

Sai da ya dafa shi sannan yasan ya shigo cikin dakin.

Juyowa yayi a Firgice. yana kallon sa. Murmushin yake ya saki. Ya ce,
"Dan uwa kai ne."

Kallon sa Khaleel ya tsaya yi, "Najib lafiyar ka kuwa."

Mikewa yayi ya kamo hannun sa. "Lafiya kalou me ka gani."

"Naje dakin Mami naga baka can, abinda ko da yaushe kana gefen Mamin ka, gashi nazo na same ka kana tunani abinda ban saba gani daga gareka ba, gashi duk naga ka rame."

"Khaleel kenan, wanka nazo nayi shi yasa baka sameni a dakin Mami ba, tunani kuma yanzu ya fado min shine nake yi, rama kuma ban dan jin dadi ne."

Khaleel ya zuba masa ido. Sannan yayi wani murmushi. Ya xe,
"Najib wanene ni a gunka."

Najib ya dube shi, "Me ya kawo wannan tambayar."

Khaleel ya girgiza kai. Ya ce,
"Malam ban amsa ta."

Najib yayi murmushi ya ce,
"Kai bababn abokina ne kuma na dauke ka a matsayin dan uwa na."

"Indai haka ne. To Dan Allah ka fadan damuwar ka, kasan nasan komai game da kai. To ban yadda da abinda ka fada min ba yanzu."

Zama yayi a kan gado ya dafe kansa. "Dan Uwa wallahi bana son ina tuno abin ne."

"Dan Allah daure ka fada min ko zan iya taimaka maka. In bazan iya ba nasaka a addu'a."

Numfashi yaja,  "Bro kasan matsala ta. ta farko, ina da bukatar aure, dan wallahi har magani ya kusan fara kin karbata,"

"Wannan me sauki ne, ka samo mata a cikin masu sonka."

Najib ya dan bata fuska ya ce,
"Kai ma kasan irin matan da nake so ai. Duk masu sona babu irin su."

"Zan tayaka nema wannan. Sai kuma me?'

"Kasan me ya kara dawon da wancan abin kuwa?"

Khaleel ya girgiza kai ya ce
"A'ah!".

Nan ya kwashe gamuwar sa da yarinyar nan da irin rashin kwanciyar hankalin da yake shiga.

Hannun  Khaleel ya kamo. Yace
"Bro, yawan mafarken da nake da ita shi ya kara kawon sabuwar sha'awar aure. Wallahi."

"Innalillahi wa'inali lahir rajiun. Bro Allah kawo mana dauki, Amman duk da haka zamu cigaba da neman ta, amman baza mu zauna haka ba, gara ka fara aure dan matsalar nan taka ta ragu."

"Anya zan iya kuwa inba wannan yarinyar ba."
"Bro kar fa dai ko gamo kayi."

Duka ya kai masa. 
"Wane gamo, mutun ce,"

"Toh Allah yasa."

Harara sa yayi, sannan yace,
"Ameen."

Dariya Khaleel yayi,ya ce,
"da kar kace Ameen din man."

"Yasu Momy da Yasmeen."
"Suna lafiya."

"Ina Anty, Suraiyya kuwa, wallahi na dade bamu yi waya ba."
"Tana nan basu dade da dawowa daga Makkah ba."

"Ina sudais din ta kuwa ya girma ko."
"Sosai ma kuwa."

"Insha Allahu kafin mu koma zan je na gaida ta."
"Allah yasa. Tinda kai yanzu mace ta dauke mana kai sai lokacin tunanin ta kake dashi baka da lokacin mu."

"Wa ya fada muku."
Sukayi dariya.

"Kai wajen Bashir zamu fa."
"Me zamuyi."

"Malam gobe fa yan mata zasuyi kamu."
"Ni nazan je wani kamu ba."

"Amman toh saboda me."
"Mata zasuyi yawa."

Driya Khaleel yayi, ya ce,
"Toh tsoron mata kuma ka fara."

"Haba dai. A'ah saboda tsaro dai."
"Kaji dashi dai. Kasan jibi dinner, gata daurin aure da kai amarya."

"Allah kaimu."
"Ameen! Tashi muje."

Najib ya mike, ya ce,
"To!"

Khaleel ma mikewa yayi
Dakin Mami sukayi.

Mami na gani su tayi murmushi. Ta ce,
"Son Ina kuma zuwa."

Khaleel ya ce,
"Zamu wajen Bashir ne."

"Sai kun dawo. Ku gaida Momyn sa."
"Zataji."

Suka fice. Tana me jin dadin ganin canjawar yaron nata. Wannan yasa take kara son Khaleel dan aboki ne na gari.

Dan taaan shi ya yi sanadin sanya yaron nata cikin farin ciki.



Summy ce zaune wajen me lalle, ana cire mata lalen da akayi mata,
Lallen yayi kyau sai kace a kafar aka hallice su tare.

Summy ba dai kyau ba, fara ce, tana da idanu sai hanci wanda yake a dan bude daga karshe.

Tana da kirar jiki me kyau, bata da tsayi, kuma jikin ta in yasamu hutu kara budewa zeyi.

Mikewa tayi ta bawa me lalle kudin sannan ta tafi saloon dan ai mata kitso.

Tana zuba zubby me mata kitso ta farai mata kirari. Tana cewa,

"Kaga hajjaju, manyan mata matar manya, matar me kyau da kudi, Allah ja da ranki, Allah yasa wannan kitson ya kawo mana miji har gida."

Ido take jutawa tana wani jijiga jikin ta.
"Ameen Zubby ya kuke ya gidan?

"Lafiya."
"Kina da attachment dai ko?"

"Eh akwai, guda nawa za ayi miki dashi."
"Kananu nake so. To ranki ya dade."

Ta bude kanta, da niyyar tsefewa. Ta ganshi a tsefe ta ce,
"A'ah Summy ya naga yau har kin tsefe kan nakki."

"Oh kedai bari, wallahi Mama ce jiya ta zaunar dani na tsefe shi."

"Toh Mama da kanta."
"Kedai bari, ita ta wanken shima."

"Mama na ji da ke."
"Tab baki san da azabar da ta wanke min bane."

"Jin fatar kaina nake kamar an tsatsaga min. Dan dirje min tayi sosai."

"Sannu."
"Yauwah. Kuma fa wai kar a samin gashi tace, ni da zamiyi biki ai dole sai an min kari."

Zubby ta ce,
"Ah gaskiya kuwa."
Suna kitso suna hira. Zuvby na kara tunzura ta.



*INDABAWA*

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now