161

738 52 0
                                    

*NAJWA*

BY *Maryam S Indabawa*
*Mans*

Dedicated to *Rashida A Kardam*
*Anty Rash*

*Allah dafa miki. Allah karawa Mama lafiya da nisan kwana. Ameen*

?? *HAJOW* ??
*Hakuri da juriya online writers*

*Allah kara mana hakuri da juriya.*
*Ameen*

*Gidan aminci da karamci. Allah kara basira Ameen*

Page
*161*

*Salma Khaleed*
Tnc for ur love. I really appreciate


Jikin sa ya janyo ta, ya ce,
"Duk laifi nane da ban fada miki tin yaushe na fara son ki ba. Sai da Zahra ta ce na fada miki amman naki. Nasan da na fada miki da duk haka baza ta faru ba."

Yai shiru ya cigaba da magana,
"abu daya zan fada miki dayan in kinaso sai dai kiji a gun wani.
Najwa nafi shekara Biyar da fara sonki, tin daga wata rana da naganni kin dawo daga isilamiyya lokacin ban san ke wace ba.
Wallahi Najwa daga kallon ki sonki ya shige ni, dan yadda kike tafiya ma nasan ke din ta daban ce, a lokacin kina rike da hannun Basma. Abinda yasa har na ganki shine an tashe ku daga isilamiyya sai aka tsaida mu dan tsalakar da yan makrantar ku.
Kuma wani ikon Allah tin da na fito nake jin wani nishadi da na rasa na menene. Abinda nasan na gani kece gaskiya Najwa nasha wahala kafin Allah ya nuna min ke.
Kullum sai na shiga gari neman ki, sau biyu na ganki da wata rana da kuka je shopping a shoprite, shima kafin na biyo ku kin bace min."

Matse ta ya karayi, ya ce,
"Wani abun mamaki shine sai gaki na naganki a katsina shima kuma kika bace min abinda yasa na dinga bibiyar katsina kenan har ranar da na ganku na biyo ku.
Mami ita na fara fadawa lokacin da na ganki, a lokacin bansan mene so ba, ita ta fara fada min ai son ki nake."

"Mamaki na dinga ganin daga kallon ki na fada tarkon son ki, bayan akwai lokacin da Mami ta ce, naje na neme ki na nuna kimin yarinta ashe akan ki nake shan wahala ban sani ba.
Ashe yaran ma sunfi wasu manyan sosai, dan ni aguna kin fiye min manyan nan mene bana samu a gunki, jin dadi kwanciyyar hankali da nutsuwa duk ina samu.
Najwa na rantse miki da Allah kice farkon wacce na fara so kinji na rantse.
Sumaiyya, Khaleel shi ya samo min ita dan yaga ya kamata nai aure, baki ga wahalar da yasha ba wannan yasa na amshi tayin sa a wajen Sumaiyya. In baki yadda ba ki tambayi Kahleel."

"Sam ban taba son Sumaiyya ba hasali ma zaman hakuri nake da ita, Sumaiyya....."
Bakin sa Najwa ta rufe da hannun ta, tana girgiza mai kai.

"Kin yadda dani, wallahi Najwa son ki ya wahalar dani. Sai yanzu nagane me yasa ya wahalar dani ashe dan zanyi babban samu ne.
Kinsan ana cewa ba a samun abu me daraja cikin sauki. To na yadda da wannan maganar ko ta kan ki ce."

"Najwa kece farin cikin rai na! Kece komai nawa. Ina sonki fiye da yadda nake son kai na. Wannan yasa na kusan zarewa lokacin da kika ce baki aure na. Yanzu kuwa kika juya baya ai nasan mutuwa zanyi kawai. Dan Allah ki rufan asiri ki janye fushin nan da kike dani, wallahi Najwa da sonki na ke rayuwa, son ki ya zama jinin jikina. Tin kafin na samu na gana dake son ki ya zama jiniin jikina.
Ina kaunar ki. Ina kaunar ki kece farin ciki na......"

Bakin su ta hade gu daya kawai, duk da rashin kwarin jikin ta haka be sa tayi sanya wajen farantawa mijin ta ba.

Sun jiyar da junan su kishirwar da suka yi kwana biyu basa tare.

Najib ya nunawa Najwa matsayin ta a gunsa, inda ba karamin Mamki abin ya bata ba.

Najib ya samu abunda yake so, Najwa ta bashi, kulawa ta kyautata masa ta kwantar masa da kishin da ta isheshi na kwana ki biyu.

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now