149

649 49 0
                                    

*NAJWA*

BY *Maryam S Indabawa*
*Mans*

Dedicated to *Rashida A Kardam*
*Anty Rash*

*Allah dafa miki. Allah karawa Mama lafiya da nisan kwana. Ameen*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya online writers*

*Allah kara mana hakuri da juriya.*
*Ameen*

*Gidan aminci da karamci. Allah kara basira Ameen*

Page
*149*

Katon gida ne gari guda, me ginin zamani. Bangare uku ne, biyu na facing juna.

Da farko da ka shiga gidan katon gate ne, sai harabar ajiye motoci, wanda yake katon gaske.

Daga can gefe wani madaidaicin asibiti ne wanda aka zuba duk abinda ake bukata.

Bangarori Biyun sune na sumaiyya da Najwa, na Najib na tsakiya.

Kowa part din sa yana dauke da katon falo sai daki guda biyu a kasa da daining area. da ban daki da kitchen, sai bene wanda shima falo ne, sai dakunan bacci guda uku a ciki.

Haka part din Najwa shima yake. Sai wata kofa dake gefen ko wanne part wanda zata sada ka da bangaren Najib.

Bangaren sa katon falo ne, sai Dakunan bacci guda uku daya kuma an zuba kayan karatu a ciki.

Dakin sumaiyya ya cika mata kaya a ciki dan duk dakunan ba wanda be zuba mata kaya ba.

Kitchen kan sa ya cika mata da kayan amfani duk da yasan ba aikin take ba.

A bayan gidan kuwa wani katon lambu ne, cike yake da kayan marmari wandanda ba rani ba damina kullim da ya'ya a jikin su, amman a tsakiyar lambun ruwa ne ke gudu. Can gefe swimming pool ne.

Sai wajen zama da akai masa wata yar rumfa, An saka wasu kujeru masu kyau a wajen. Duk gidan an kawata shi da fulawoyi abin sha'awa.

Gidan gaskiya ya gaji da haduwa dan duk abin more rayuwa an saka a ciki.

************
Sumaiyya kuwa tinda Najib ya tafi biki suka daga Niger dan samun yadda zasu da taimako.

Hakuri bokan ta ya bata, sai bayani akan magani da zai bata tayi amfani da dhi. Ya za a dace akan sa.

Zai yi aiki ne akan duk lokacin da Najib zai kusanci Najwa bazai iya ba, zai zamar mata kamar mace. Hakan zai sa ta gaji ta fasa auren.

Sumaiyya ba karamin dadi taji ba dan haka ta tafi da murnar ta dan tasan duk amaryar da ba'a kusan ce ta ba na wasu lokutan dole ta hakura da auren bama in tayi tunanin haka yake dole a fasa auren.

Da karfin gwiwar ta ta tafi tana jin dadin nan da wasu lokuta zata rabu da Najwa. wannan yasa ta sa a ranta zata nuna bata da wata damuwa akan auren bare a gane akwai abinda zata gudanar nan gaba.

Tana komawa gida ta kira Najib a waya abinda yai matukar bashi mamaki kallon screem din wayar yayi har wayar ta katse ta kuma kira. Dagawa yayi cikin sanyin jiki dan besan me zata ce masa ba ko ba lafiya ne.

Dan  yasan Sumaiyya inda ba shi ya kira ba ko za a mutu baza ta kira shi ba.
"Assalamu Alaikum!"

Ya Fada, da "Hello!"
Ta amsa masa sallamar. Wannan ya kara tabbatar masa da Sumaiyya ce dan sam Sumaiyya ba ruwan ta da Sallama.

"Ya aka yi ne Sumaiyya?"
"Lafiya daman na ce yau za'a kawo amarya ba abinda za'ayi ne."

"Toh!"
Ya fada a ransa yana dauke wayar a kunnen sa dan kara tabbatar da menyin magana.

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now