160

738 55 0
                                    

*NAJWA*

BY *Maryam S Indabawa*
*Mans*

Dedicated to *Rashida A Kardam*
*Anty Rash*

*Allah dafa miki. Allah karawa Mama lafiya da nisan kwana. Ameen*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya online writers*

*Allah kara mana hakuri da juriya.*
*Ameen*

*Gidan aminci da karamci. Allah kara basira Ameen*

Page
*160*

*Godiya me tarin yawa ga masoya littafin nan. Nagode Allah bar kauna.*




Sai karfen tara ya baro gidan Mami bayan ya amsowa Najwa kwadon ramar.

Yana zuwa gida yai mata knocking ta fito ta amsa yayi bangaren Sumaiyya.

Tana zaune a falo, kamar yadda ya fita ya bar ta.

Yanzu ma ko kallo bata ishe shi ba, Haka ya karaci zaman sa ya mike, yayo wanka ya saka kayan baccin sa.

Fita yayi, ya yi bangaren Najwa. Najwa na zaune tayi dai dai da ita daga ita sai ves da wani wandi three quater.

Kanta ba dan kwalli tayi parking nashi, gaban ta farantin rama ne, har guda biyu.

Daya take ci, dayan ta rufe shi, sai maltina da ta dauko zata sha.

Yana shigowa ta kalle shi da murmushi akan fuskar sa,
"Baby na ni ina tawa."

"Taho muci."
Mikewa yayi ya zauna suna ci.

Sai da taji tayi nak, sannan ta mike ta shiga kitchen din ta, lemon kwali ta dauko masa sai snacks din da tayi dazu.

A faranti ta kawo musu, meat pie kawai ta ci ta dauke hannun ta.

Najib kuwa tinda ya fara ci ya kasa daina ci duk da cikin sa a cike yake.

Tinawa da yai ba lallai ne ya samu break gobe ba yasa, ya ce, ta ajiye masa sauran gobe zai amsa in zai je office.

Kwashe kayan wajen tayi, daya plate din zogalen ta saka a friji dan kada ya lalace, komai ta maida shi inda yake.

Falo ta koma, kallon ta yayi, ya mikar da ita, ya ce,
"Muje nai miki wanka dare yayi."

"Toh!"
Dauka ta yayi, sukai sama.

Sai da yai mata wanka sannan ya shirya ta cikin kayan baccin ta.

Kan gado ya kai ta, ya kwantar da ita. Kallon ta yayi ya ce,
"Baby mun tsara yadda kwanan girkin ku zai kasan ce. Kwana bibiyu ne, sannan da safe da rana da dare duk zan na shiga dakin 'wacce bata da girki dan naga halin da take ciki. Yayi."

Kai ta sunkuyar ta ce,
"Duk yadda kuka tsara yayi."

"To Allah miki albarka."
Da "Ameen!"
Ta amsa.

Sai da yai mata addu'a sannan ya rufe ta da bargo. Kissing nata yayi sannan ya mike.

Fitilar dakin ya kashe, ya fita, ido ta lumshe tana jin kewar Najib.

Tasan Bacci barawo ne zai dauke ta, inda ta saba kwana a jikin Najib yana ririta ta, yau gata daga ita sai fulalluka. Duk wanda taja dan taji dadi amman sam babu.

Da kyar tai bacci, wanda zazzabi ya tashe ta cikin dare.

Rasa yadda zatayi tayi. Gata ba gwanar shan magani ba. Haka ta gama rawar jiki har bacci ya dauke  ta.

Gefen asuba ta tashi, alwala tayi dai dai lokacin da Najib ya kirata.

Dauka tayi muryar ta a sanyaye, ta ce,
"Hamma na tashi."

NAJWA Complete ✔Wo Geschichten leben. Entdecke jetzt