96-100

636 61 0
                                    

*NAJWA*

BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*

PAGE *96-100*

DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTU RASH KARDAM*


Kamar ko da yaushe, sun dawo daga makaranta tare da kanwar ta, hannun su rike da na juna.

Kanta a kasa take tafiya dan ta tsani kallo. Duk da ta saka Nikaf.

Basma ta take tayi mata surutu. Hannun ta, ta rike.

Shiru Basma tayi. Sai da suka shiga cikin gidan su sannan ta kalle ta.

Ta ce,
"Haba Basma sai kace ba mace ba. Mace fa an santa da yanga da jan aji. Amman muna tafiya kina ta surutu."

Kallon ta Basma ta tsaya yi. Basma tana son Yayar ta, kuma tana burgeta kome nata a tsare da hankali take yin sa.

Idon ta *Najwa* ta hure da bakin ta.

"Tunanin me kike ina miki magana?"

Murmushi Basma tayi, sannan ta ce,
"Wallahi Adda kina burge ni."

Murmushi itama *Najwa* tayi, ta ce,
"Shige muje daga ciki."

Suka shige bayan sun gaida Baba Me gadi.

Mami kamar kullum na zaune akan sallaya tana lazumi.

*Najwa* ce ta fara mata sannu da gida sannan Basma da ta haye kan kafar ta.

Kallon ta *Najwa* tayi. Ta ce,
"Basma kedai bakya girma tashi muje ki cire kaya kiuo alwala."

"Toh."
Basma ta fada tana mikewa.

Bayan *Najwa* tayi da tayi bene.




Zaune yake gefen Mami yana aiki cikin laptop dinsa.

Sanye yake da dogon wando, baki, sai farar riga me dogon hannu, idon sa sanye da gilashi. Sai tashin kamshi yake. Ke kace unguwa zashi ko wajen budurwa.

Mami ce ta mika masa lemin da ta tsiyaya masa a kofi.

Karba yayi ya sha. Sannan ya ce,
"Mami gobe ne fa mothers even din Mamin Bashir."

"Ban manta ba. Allah kaimu. Zaka kaini ai."

"Momyn Khaleel ma zata je fa."

"Ah toh ai da sai ka. Kaimu gaba daya ko."

Kallon Mami yayi,  "Kinsan kuwa ranan ta zo."

"Yaushe?"
"Ranar da mukaje gidan su Abbah."

"Amman ban ji dadi ba. Gashi ni ban je mata ba."

"Ran juma'a na kai ki ki wuni, tinda sai Monday zamu tafi."

"Allah kai mu, ranar asabar zanje gidan, Ummah, lahadi naje wajen su Mamah."

"Ummah kuwa ta ce, naje tayi min dambu."

Fuska Mami ta bata, "Najib ka kiyaye ni fa da sa min iyaye aiki wallahi."

Dariya yayi, ya ce,
"Haba Hajiyata. Ina wani aikin yake."

Fuskar ta a hade dai. "Baka ji ko?"

Dariya ya kuma yi. Ya ce,
"Yi hakuri da wasa nake, yimin zata bayar ayi."

Murmushi tayi, "Wai Najib ka mai dani kakar ka ne ko?"

Ido daya ya kanne, ya ce,
"Toh ya zanyi tinda kin hanani jan kakan nin nawa."

Murmushi tayi ta dauki remote tana canja channel.

Shirun da suka samu, yasa ya lula tunanin Yarinyar da ta hanashi sukuni. Wacce kullum sai yayi mafarkin ta.

Kullum tana cikin ran sa. Be da buri da ya wuce ya ganta. Ajiyar zuviya ya sauke. Sannan ya cigana da aikin sa.

A ransa yana mamamkin yadda Allah yasaka masa son wacce be santa ba daga kallo.

Lalle ya kuma jin tsoro da kara gaskata lamarin Ubangiji.

Parking mota yaji ana yi. Labulen dakw gefen sa ya daga. Murmushi ya saki. Yana mikewa.

"Mami gasu ango nan."

Itama Murmushin tayi, dai dai lokacin da suka shigo dakin tare da Khaleel kenan.

"Mami ina yini?"
Bashir ya fada yana dukawa har kasa.

Cikin fara'a maami ta amsa masa,
"Lafiya lou yasu Monyn taka."

"Murmushi yayi, ya ce,
"Suna lafiya."

Khaleel ne ya koma kusa da ita, ya ce,
"Mami ina yini?"

"Lafiya lou Khaleel. Yasu Momy taka."
Ta amsa masa,

"Suna.nan kalou."
"Ashe ranan tazo ba ma nan."

"Wallahi Mami."
"Wallahi kaga yaron nan sai yanzu yake fada min ma."

kitchen taje ta sa Jummala ta kawo musu lemo da abin tabawa.

Sannan ita kuma tayi bayan gida.

Jummala ce ta kawo musu lemo, da nama da meat pie a gefe.

Najib ne ya tashi ya zuba musu lemon a kofi, sannan ya kuma ya zauna.

Kallon Bashir. Ya ce,
"Ango Ango."

Gira Bashur ya dage masa, ya ce,
"Kai dai bari na kusa shiga sahun manya na barku abaya."

Khaleel ne yayi dariya, ya ce,
"Mu dai barshi."

Hararar sa Najib yayi, "Mene a ciki to."

"Ai kam da komai a ciki. Malam zamu samu nutsuwa mu kara hankali fa."

Dariya Najib yayi, ya ce,
"Da baka da nutsuwa da hankali ne."

Murmushi Khaleel yayi, ya ce,
"Malam ba irin wacce kake tsammani ba ce."

Bashir ya ce,
"Yauwah aboki fada masa dai."

Dariya Najib yayi, ya ce,
"Malamai bana son iska ci kuma."

"Ina jin fa Najib be da lafiya ne."
Bashit ya fada da tsokana.

Dariya Khaleel ya sheke da ita.
"Tab wannan ai duk nan ya fimu lafiya in dai ta wannan fannin ne, na fada maka yanzu magani ma yana son daina karbar sa."

Folon dake gefen sa ya dauka ya cilla masa.

Karewa yayi yana dariya ya ce,
"Karya nayi ne?"

"Wallahi Bro sai nayi maganin ka."

Driya Bashir yayi, ya ce,
"Toh ko sai mun nemo masa mata ne."

Dariya Khaleel yayi! Ya ce,
"Ai shi macen da yake nema daban ce."

Bashir, ya ce,
"Ka fadan wace iri ya yake so. sai mu samo masa."

Najib ya rufe laptop din gaban sa, ya ce,
"Malamai bana so. Kasan kai ma na samu ai."

Driya Khaleel yayi, kawai. Ya ce,
"Ku tashi muje."

"Ina zamu,"
Najib ya tambaya.

"In munje ka gani."
Khaleel ya fada masa.

"Nifa banson yawo."
Najib ya fada

"Tinda Allah ya hadaka damu ai sai kayi hakuri."
Khaleel ya fada yana mikewa.

Shi dai Bashir dariya kawai yake., dan Najib da Khaleel na matukaw burge shi.

Bayan gida suka nufa inda Mami ke zaune.

Sallama sukai mata sannan suka fice.

*INDABAWA*

NAJWA Complete ✔Where stories live. Discover now