Babi na arba'in da uku

9.5K 910 84
                                    

*Bismillahir rahmanir rahim*

*fazakkir fa innaz zikra tanfa'ul mu'uminin*

*_KA TUNATAR DOMIN TUNATARWA TANA AMFANAR DA MUMINI_*

_______________________________

         Nan gefan abdallah ya kwanta yana ci gaba da kuka tamkar wani qaramin yaro,jin zuciyarsa yake kamar zata fashe,janyo abdallah yayi cikin jikinsa yana magana qasa qasa mai cike da kalmomin nadama yana ci gaba da kuka.

          Sai da rana ta soma bugun naman jikinta sannan ta iya miqewa a daddafe ta yafa mayafinta,takalmi kuwa basu sakuwa a hannu ta riqesu hadi da jakarta,da qyar da jan qafa ta kai kanta titi ta tari adaidata sahu ta hau duk da cewa bata da qwadalar da zata bashi,qofar gidansu ya sauketa tace ya jira ta miqo masa kudin,tana sallama ta zube a tsakar gidansu tana maida numfashi,mamarta dake wanki bakin fanfo ta dago tana dubanta,mamaki ya cikata saidai bata da ikon tambayar ta abinda ya sameta,murya can qasa da qyar ta qwalawa qanwarta kira
"Idan akwai naira dari jakarki fita waje ki bawa mai adaidaita sahu,mama dora min ruwan zafi" kowannansu da to ya amsa mata,maman ta saki wankin ta shiga kitchen.

      Gashi tayiwa kanta sosai tamkar kai jego,tanayi tana runtse ido zuciyarta na zafi da quna,tana tuna yadda mukhtar ya dinga jibgarta kamar wanda ya sayi jaki mai taurin kai,dakinta ta koma ta shafe jikinta da man zafi ta samu ta kwanta sannan ta janyo wayarta tayi kiran abokiyar shawara da shaidancinta zinatu,tana dagawa ta buqaci ganinta,cikin sa'a kuwa tana kusa.

      Cikin mintuna qalilan zinatun ta iso,suka gaisa da maman wanda ke zaune tsajar gida tana shirin dora abincin rana,da kallo tabi zinatun har ta shige dakin,
"Lafiya?,na zaci zaki cemin gaki gidan mukhtar anyi kome sai nazo na sameki kina tashi da qyar haka?"baqinciki ya sake tokare zainab,cikin bacin rai ta soma fadin
" ni malam zai ciwa kudi zinatu,ni zai ha'inta?,kalli jikina ki ga abinda mukhtar ya yimin duba zinatu"
"La la lal" shine kawai abinda zinatu ke fada tana gyada kai
"Garin yaya haka zainab" tas ta kwashe yadda komai ya faru ranta na quna ta qunduma ashar sannan ta dora
"Ba sai na warke ba gobe gobe zamu koma wajen malam,wallahi sai na nuna masa ni 'yar tasha ce,duk abinda ya buqata nayi masa,kwana nayi yana sasukata duk warin dake tashi a jikinsa amma ban damu,shine ni kuma zai rainamin wayo an gaya masa ni gara ce,to wallahi Allah ya nuna mana gobe shege ka fasa" haka ta dinga bambami zinatu na tausarta da haka sukayi sallama da niyyar gobe da sassafe zasu dirarwa malam

  *******  *******   ******

       Tana zaune bakin gadonta tana ninke kayan sawarta a hanakali,tunanin abdallah na kai komo cikin ranta tun safe,tunda ta haifeashi basu taba rabuwa daidai da kwana guda ba banda sanda ta yayeshi sai wannan lokacin,yanzu haka watanni kusan shida kenan bata sanyashi a idanunta ba,gidan nasu yau shiru yake tun safe har yammaci,hajiya na bangarenta yau bata jin dadi,tunda ta kammala mata girki sai ta barta ta dan kwanta ta huta,karima ta hada kan yaran sun tafi sunan qanwarta data haihu,bata kuma bar nuwaira ba haka ta kada ta suka tafi tare,yaran baki daya sunci ado banda ita,a haka da sauqi tunda sumayya ta tattara dukkan yagaggun kayanta ta boye ta hanata sakasu tafiddo mata da wasu,haka karima ta haqura bayan sa'insar da suka sha da sumayyan,a yanzu bata da goyon bayan hajiya lukman kuma bai gari yayi tafiya bare ta hadata da shi.

        Hudu da rabi na yammacin taji sallamarsa bakin qofar dakinta,a hankali ta daga kanta tana dubansa,ta mance yaushe rabon data sanyashi a idanuwanta tun kafin yayi tafiyar nan wadda ita kanta satinsa biyu kenan baya nan,sanye yake da shadda dinkin tazarce da hula saman kansa sai takalmi sau ciki,kafadarsa rataye da jaka ta matafiya,kallonta yake yana mata murmushi
"Sannu da zuwa" ta fada tana gyara daurin dan kwalinta
"Yauwa sumayya,ya gidan?" Ya fada yana zama gefanta yana mai ci gaba da kallonta
"Lafiya qalau" ta fada tana hada kayanta waje guda tare da miqewa ta zura hijabinta tana shirin ficewa
"A'ah,ya haka kuma,ya zaki fita ki barni"
"Au da dawa nake barinka" ta fada tana gyara zaman hijabinta gami da kallonsa
"Amma dai ai yau gidan babu kowa ko?,wa zai kula da ni?"
Qugu ta riqe tana duban idanuwansa
"Sai babu kowa cikin gidan sannan nake da amfani a gunka?,to gun hajiya zani na dubata na barota bata jin dadin"damuwa qarara ta gani ta bayyana kan fuskarsa karo na farko kan maganar da ta shafi mahaifiyarsa
" subhaballahi tun yaushe?,muje na ganta"ya ajjiye jakarsa ya miqe yabi bayanta.

KUNDIN QADDARATAWhere stories live. Discover now