Babi na tamanin da shida

20K 1.6K 624
                                    

*Bismillahir rahmanir rahim*

*Allah madaukakin sarki yana cewa*

*haqiqa muminai 'yan uwan juna ne kuyi sulhu tsakanin 'yan uwanku*
_____________________________________

Qarfe uku saura na rana suna zaune bayan motar driva na jansu,tattausan tafin hannunshi na cikin nata,yana zaune gab da ita sabanin daa da kowa ke zama tashi shiyyar,kunya ta sanya ta maida kanta bangareb window tana duban hanya cikin baqin glass din da motar take da shi,yatsunsa ya sanya ya juyo da fuskarta gareshi,ya dage gira daya
"Ina son miki qari kan abinda na fadi miki dazu,zayyano min naji kin haddace?" Wata iriyar kunya ta kamata,ta yaya zata iya maimaita kalaman dazu masu nauyi da girma,kanta ta qwace daga hannunshi ta sake maida kanta ga window murmushi na son kubce mata,ganin haka ya sanyashi janyota jikinsa ya sanya hannu ya matseta
"Maganinki zanyi,naga alama baki fara daukan lacture ko daya ba,yadda nake daban haka nakeson matata ta zama ta daban,you must be ready,qarin karatu guda daya,dole ki koyi zama a jikina,bazan lamunci zama a mabanbantan wurare ba ba,idan baki son haka ki daina zama waje daya da ni" ya fada yana shan mur,baki ta murguda wanda yayi nasaran hangota,cikin zuciyarta tana mita,wuta ce ta dauke mata sanda taji hannayenshi cikin rigarta,ta daga kai ta dubeshi tana narke fuska,idanunshi lumsassu ya zaro mata waje yana mata nuni data daina kallonshi,tilas ta sauke qwayar idanunta,tana ji tana gani haka ta haqura ya dinga yadda yaga dama da ita,sai da yaji tsaiwar motar sannan ya zare hannunshi da jikinshi,hannun nasa ya sanya ya gyara mata rigarta da yafen mayafinta,wanda atamfa ce a jikinta ta dora mayafinta saman ka,kanta na a qasa cike da jin nauyi har ya kammala,bata dago ba sai da taji yace
"Oya,lets go".

Tayi zaton ganinta a airphort sai ta gansu cikin wani makeken guri wanda yaso yi mata zubi da gida,mutane ke kai kawo,kama daga qananun yara saffa saffa da kuma manya,yana fitowa wasu tarin ma'aikata suka qaraso wajem,cike da girmamawa suka tarbeshi,a mutunce yake gaisawa da su,sannan ya saka hannunshi cikin na sumayyan sanda suke masa rakiya zuwa cikin wani babban gini dake gabansu,ta daga kanta a hankali a naj taci karo da wani rubutu cikin manyan haruffa daga saman gidan wanda aka rubuta MUHAMMAD ALMUSTAPHA ORPHANS HOUSE,cikin ranta take rayawa gidan marayu dama gareshi.

Babban office aka bude wanda shine mallakinsa,office din nada girma qwarai,akwai kyau tsari da wadatar tsafta ko da yaushe,sun sani haka yake,ya saba kawo musu ziyarar ba zata,sai a gama waya da shi yau anjima ku ganshi cikin gidan,duka yana haka ne saboda ya tabbatar kowa ya riqe amanar aikin da aka bashi,saman doguwar kujerar cusion suka zauna shi da ita kafin su shiga gaisawa da wadanda ya dorawa nauyi da alhakin kula da gidan,cikin nutsuwa da sanin aiki kowa ke masa bayani kan nashi bangaren da yake riqewa,kusan mintina talatin kafin ya buqaci kewaya fadin gidan.

Hannunshi tsam cikin nata tafin hannunsu a hade,kunya duka ta kamata,baijin kunyar jama'ar da suke tare?,eanda ta lura wasu sai satar kallonsu suke,a hankali suja fara kewayawa bangaren makarantar yaran inda suke karatu,makaranta ce mai zaman kanta,nursery primary zuwa secondry duka cikin gidan suke,bangaren wajem wasannin yara daga cikinsu,gurin koyon sana'ar manya,da dan madaidaicin asiniti don duba lafiyarsu,duk inda suka zo wucewa suka ci karo da wasu idan manya ne sukan qaraso fuskarsu dauke da madaukakiyar fara'a,abinda zai baka mamaki yadda suke bashi hannu kai tsaye suyi musabaha cikin yanayi na sabo da jan mutum a jiki,idan mata ne sukan duqa cikin girmamawa su gaidashi su wuce suna murna,yara qananu maza da mata da gudu suke qarasowa wajensa,yakan daga su ya sumbacesu,ko ya shafa kansu idan sunyi girman da zaya dagasu,idan yaga wani cikin yanayin da bai masa zai tambayi ba'asi ko dalilin barinsa haka?,bare ma da wuya kaga wani cikinsu cikin mummunan kama,kowa neat yake cikin tsafta da tufafi mai kyau,tun tana satar kallonshi ta gefan idanu har ta koma ta gaban idanuwa,karon farko da taji ya burgeta a rayuwa,wanne irin mutum ne shi mai tausayi haka,sauqin kai jin qai da son yara?,yadda yake mu'amalantarsu abun yayi masifar burgeta,ko banza tana da maraya,tasan ciwon rashin uba,bare wadaj nan da ba'a rasa yaran da ake kira shegu a cikinsu,wanda basu da kowaba duniya,an yardasu tun suna da qananun shekafunsu,basuji ba basu gani ba,ba'a barsu da tabin da aka haifar musu ba na rashin fitowa ta hanyar data dace ba,sai da aka sake cika rayuwarsu da tabo da quncin rashin sakin waye uwa uba kuna dangi a garesu,ba shakka yayi wani abu mai girma arayuwarsa wanda koda shi daya yayi a duniya ya cimma nasara,ma'aiki S A W yana cewa 'nida mai kula da maraya kamar haka muke a aljanna(sai ya kwantanta da yatsansa dan manuni dana tsakiya)' me yafi wannan alkhairi na zama maqoci a aljanna wajen fiyayyen halitta?,ba sai kayi da yawa ba,ko guda daya ka kula da shi kana da wannan garabasar bare kuma kayi serving rayuwar daruruwa,koda baka jin rahama da tausayi cikin zuciyarka kana jinta kamar a qesashe ka dimanci shafa kan maraya kamar yadda ma'aiki ya umarci wani sahabi,Allah ka bamu iko ka bawa masu ikon da qargin cikinmu ikon taimakawa marayan.

KUNDIN QADDARATAWhere stories live. Discover now