Babi na tamanin da hudu

19.6K 1.1K 187
                                    

*Bismillahir rahmanir rahim*

*Allah madaukaki yana cewa*

*HAQIQA ABINDA AKE YI MUKU ALQAWARI/ALWASHI(NA ALQIYAMA)MAI ZUWA NE,KU BA MASU TSEREWA ALLAH NE BA*

Allah ka sanya farinciki a zukatanmu a wannan rana,ka sanyamu qarqashin inuwarka.
_____________________________________

*WANNAN SHAFI SADAUKARWA NE GAREKU,HAQIQA ALKHAIRINKU GARENI BAZAN MANTA BA*

*SISTER AINA'U(HUGUMA CONVERSATION)

*TASH (INSPIRING STORIES GROUP)*



Hannu biyu ta sanya ta karbi rigar tana kauda kai daga kallon da yake mata wanda sam bata sonshi,yana sanyata jin wani irin abu da nauyi cikin jikinta
"Inji hamza" ya fadi yana juyawa gaban madubi yana ci gaba da taje sumarshi hankali ta furta
"Na gode,Allah ya saka da alkhairi" bai amsa ba saici gaba da kallonta da yake ta cikin mudubi,bai tsammaci jin wata addu'a ko godiya daga bakinta ba,don hamzan yasha yiwa su'ad kyauta wanda ta ninninka haka saidai ta karba ayatsine,wani lokaci idan ta duba ma takance
"Shikam baisan me yasa bai iya kyauta ba,yana qarqashun mijina yana aiki yana cin arziqinsa ya rasa mai zai bani sai wannan?" Harara yake jifarta da ita almustaphan sannan yace
"Ki shiga hankalinki su'ad,hamza ba aiki yaje qarqashina ba kafada da kafada muke aiki,ba tilas sai ya miki kyauta ba don ba qasanki yake ba,ki gyara bakinki" hakan na mata ciwl,don ita a duniya ba abijda ta tsana irin a daidaita matsayinta dana wani,wanin ma dake gain kamar bai isa komai ba.

Wayarshi ce ta fara tsuwwa,ga zatonshi ma umme ce zata ce ya hadata da sumayya,saboda haka bai ko dubaba ya daga yana karawa akunnensa,ya maqaleta a kafadarshi yana ci gaba da shafarshi,muryar su'ad ce cikin bacin rai da kwantar da murya cikin harashen nasara
"Ashe da gaske ne abinda akefadi idan namiji yayi aure wulaqantaki yake?,yanzu a haka kakeso na yarda na karbi kishiyar da ka yimin mu zauna tare?"shiru yayi tamkar bai kam layin har sai data kira sunanshi,kawai sai ta saki kuka harda sheshsheqa,cikin harshen hausa da son dawo da qauna cikin zuciyar wanda kuke magana tace
"almustapha kasan duk duniya babu wani abu da nake qauna sama da kai don me zaka yimin haka?"
"Look su'ad,wannan baki daya matsalarki ce ni ban da case da duka zantukanki,i think na gaya miki dukkan wani rules nawa ko?,so pls idan zaki iya bi bismillah,if not ki qyaleni na huta hakanan"
"Ni kake wulaqantawa haka maan?"cikin fushi yace
"if u dont like how things are,take control,decide how u ar going to change it,kada ki sake nema na daga yau,take me as iam,or leave me as iam"katse layin yayi ya jefa wayar gefanshi,cikin bacin rai yaci gaba da shiryawa sauri sauri,sumayya kam tunda taji ya ambaci su'ad ta miqe ta shige toilet,dama wanka take sonyi wanda yau bata samu tayi da wuri ba tun na safe da tayin.

Cire wayar su'ad tayi daga kunnenta sanda ta fahimci ya katse kiran nata,duk da ba yau ne farau ba idan tazo masa da shirme amma wannan yayi matuqar baqanta mata,gani take kawai saboda ya sake aure ne ya sake qaro wulaqanci fiye da wanda ta sanshi da shi,hawaye na bin idanuwanta ta dubi mamanta,sannan ta dubi qanwar maman nata anty kubra dake zaune tana kallonta wadda ke zaune ita mijinta a south africa,ta zo ne american wajen yayarta ta tadda wannan cakwakiyar
"Ba sai kince komai ba naji komai,ai wallahi laifinki ne khaulat,ta yaya har zaki bari su'ad tayi wasa da damarta,kunfi kowa sanin samun damar auren irin su mustaphan sai wanda Allah ya zaba nan gidan duniya,tun tuni kallonku kawai nake,yarinya tana gantalinya da sunan karatu,karatun uwar me?,me zata ci da karatun?,me take nema da shi?,dame mijinta ya rageta?,bata taba tambayarsa abu komai yawansa yace mata babu ko bazai bayar ba saidai ma ya ninka mata,kuna zaton miji irin mustapha wanda Allah ya yuwa baiwar kyau da kudi zai zauna bai sake aureba bayan yana da mace irin su'ad?,to ta godewa Allah ma daba neman mata yake ba ya kwaso wata cutar ya laqaba mata,kinga idan zaki zubar da wannan gantalallen karatun naki kije ki kwashu makaman qwatar mijinki kije ku buga ke da ita mai rabo ka dauka to,ta taki qatuwar sa'ar samun auren elmustapha bayan gwagwarmayar da aka sha,duk da tasan cewa ba sonta yake ba amma tausayi da qaunar da take masa ya sanya ya amincewa aurenta" ta fada tana maida numfashin takaici
"To kuma kubra me ya kawo tonon silili haka?,abinda ya wuce ai ya riga ya wuce ko?,kawai shawara muke da buqata"
"Ki tattarata ta koma gidanta,ko a kango yace ta zauna ba nijeria ba ta zauba,bare ma meye marabar gidan nata da nan din?don kawai tana cikin family house,kowa ya sani qaryarka kace gidan mutum kamar almustapha an rasa jin dadi da walwala da dukka wata qawar duniya,idan zata koma taje kowa ta qwaci mijinta to,idan kuma zama zatayi bismillah saikici gaba da dorata akeken bera ki kuma share mata wajen zama,kinsan dai ko auren ta kaso wallahi duk yadda takejin kan nan nata a sama ba zata samu wanda ya koda kama qafar doctor mustapha ba"
"Ya isa kubra don Allah,ke dole sai kin zagi mutum zakiji dadi" waiwayawa haj khaulat tayi ta dubi su'ad dake zaune hawaye shabe shabe,har cikin qirjinta taje jin kishin mustapha,tamkar ta dauki ran wadda ta aure mata shi haka take ji,kullum kwanan duniya ji taje kamar ta yanki ticket ta koma masa,don tun kafin a kai ko ina ta soma raina kanta,ta tabbatar rabuwa da mustapha kamar yadda tayi iqirari ba mi yiwuwa bane a rayuwarta,ko sakinta yayi tana jin ba zata iya qara aure ba har ta mutu,don gani take nan duniya babu kamar yashi
"Zaki shirya ki koma wajen mijinki,daga yau so nake kada ki saurara kada ki daga qafa,duk inda ya sanya qafa ki bishi,sai kin tabbatar kin mamaye rayuwarshi,sannan cijin gidan bance ki saurarawa uban kowa ba,fin baki dayansu munafukai ne,suna da masaniyar qara auren nasa su suka hada,ki taka uban kowa koda kuwa hajiya zuwairiyya ce uwarsa kinji na gaya miki,ki fara shiri,naji labarin biki ya tasi a gidan,zaki isa ranar daurin aure don kiga idon uban kowa,uban kowa yaga naki idon ihee"kai su'ad ta gyada cike da gamsuwa da samun qwarin gwiwa,itadai kubra na gefe tana kallonsu tana tabe baki,ta tabbatar zamansu bazai taba daidaita da mustaoha ba matuqar tace zata taba iyayensa,kai ta dauke tana qissima yadda dramer zata kwashe.

KUNDIN QADDARATAWhere stories live. Discover now