mijin tsohuwa (4)

666 52 2
                                    

Dakinshi ya nufa ya kintsa shidai ba wani girki halima take mashi ba kuma ta soni sarai baya iya cin girkin masu aiki se koya yayi dole.
Ya shiga kitchen ya hau feraye dankalin turawa se jin mutum yayi tsaye a bayan sa. "kai malam bayan wannan dubu darin ka turon 4.2 don ni nan daka ke ganina na wuce se kuma bayan wata 7" shuru yayi yana kallon ta cike da mamaki "ina kuma zaki" yayi nuni da trolley in data rike a hannu. Tsaki taja "dubai zani, na riga da na sai ticket nayi booking hotel tin tini"

"Wa kika tambaya?"

"Thooooo idan bazaka turon ba ni na san yadda zanyi" halima ta kyalkyale da daria ta juya zata fita "haba halima, ya kamata kina tambayana idan zaki fita" "Thom kashe ni zakayi idan na fita ko kuma me? Ko'an gaya maka tsoron ka nake ji?"

"No, i mean sabida fushin Allah, nidai muje in raka ki. Amma karki kuma shirin zuwa ko ina ba tare da sani naba" ya fada yana ajiye wukar gefe "aikin banza aikin hofi? Are you threating me?!" Ta fada cikin daga murya tana nuna shi " idan fa ka matsamin wallahi tallahi barin gidan zanyi na barka" har ya fara harzuka kawai ya dane ya kyale ta, dan idan ya biye mata ba wanda zeji dadi. "Idan kika tafi ba se na zauna da maid inki ba" ya furta da niyar zolaya

Tasa kafa zata fitta ta furta ciki ciki yadda tasan zeji da ta " ko me nakashashen dan adamu ze iya oho ni dama ze iya da har marigayin seya ji dadi" we ita a lallai seta mayar masa da magana.

Ran abubarkar in yayi dubu thom ya baci, ji tayi an daka mata tsawa kamar daga sama "keee idan kika bari kafarki ta haura bakin kofa thom wallahi kar ki kuskura na kara ganin ko innuwarki a cikin gidan nan!" Ya juya a fusace ya shiga daki.

Halima ba kadan ta girgiza ba Dan kaf shekaru 13 da sukayi tare be taba nuna bacin ranshi ba se yau

Shahara (Hausa Love Story)Where stories live. Discover now