kadara ce (1)

481 44 6
                                    

"ka yafe mun" ta kara maimai tawa kamin ta sake shi. kallo ya bita da shi har lokacin kuka na fita daga idon shi a hankali.

fara'a ta danyi mishi ta ja hannun shi suka kara sa ciki ta turo kofa. har lokacin ita yake wa ido.

"fahd zo muyi hira" ta ce dashi sannan ta zauna akan gadon.

wuri ya samu ya zauna a gefen ta sukayi shuru... chan yaji tana dariya
ya juyo yana kallon ta.

"ka tuno lokacin da kadan gare ya tarfa mu a ban daki?" ta fada cikin dariyar tata. shuru yayi yana tunowa
chan ya ce "wani baki mara jela... me kama da...."

rufe masa baki tayi "rufa min asiri kaji" murmushi yayi ya gyada kai.

sun dade suna hira su biyu suna tuno abin daria da na haushi. ita umni ma bata san wasu abubuwa wan ba se lokacin.

"fahd... kasan wani abu..."

girgiza kai yayi. "ina so... ko me zaya sa me ka... idan ba ni ba... kar ka fada ma kowa. kada ka taba bari wani ya gane bacin ranka" ta kwantar da kanshi a kan cinyar ta tana shafa masa sumar shi a hankali

"ka yarda komi kaddara ce ama... kada ka bari wani ya danne ma rayuwar ka... ko ya zakayi kayi kokari ka yi karatu me kyau dan ka daukaka... nasan kana da illimin addini sosai dan haka ka dinga addu'o i ... baka da wani aboki se qur'ani... kaji..."

"uhm......" kawai ya ce kamin bacci ya dauke sa.

be bude ido ba se wurin 2:30 na yamma.

furgit a farka gaban sa na faduwa. tuno maganar da sukayi da umni yayi kamar a mafarki...

nagode

Shahara (Hausa Love Story)Where stories live. Discover now