💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗AYSHA A BAGUDO
Page 19-20
Shiyasa kaga bazan iya kai" kaina gareta ba da sunan Ina sonta , bare tamin salo .
Nan km yayi ta zazzagawa Fk maseefa hade da cewa ai shi yaja masa duk wulakancin da'aka masa .
Fk yace kwantar da hankalinka kabarni daita kawai ,nasan zata yarda ma ,.
kawai dai itama so take ta nuna mana ,itama macece , nasan jan aji ne kawai na mata Amman ita din wa dazatace bata sonka ,Ina rai inshallahu zamuyi nasara.Cikin fushi da jin haushi deeni Yace in taki yarda ka kyaleta kawai , yarinya sai kace wata gold sai wani yawo akamin da hankali akanta, yaja tsaki hade da kashe wayar batare daya sake jin abinda fk zai ce ba .
Kwana deeni yayi da tunanin hade da zullumi halin da zai tsinci kansa idan yarinyar nan taki yarda dashi, duk shi Gani yake ba sonta yake ba. zai dai yi aure ne kawai saboda umarnin umminsa, bugu da Kari ma, bazai iya kaskantar da kansa wajen mace ba ballanantana har ya kai shi ga furta kalmar so.
Har zuwa wayewar garin ya cigaban mamakinta ganinta yake , tamkar yau aka haifeta, sannan har zuwa yanzu kallon karamar yarinya yake mata, ashe tasan abinda take yi ,uhmmmm uhmmmm ahankali ya dinga sauke ajiyar zuciya, wai zatayi tunani akai ya sake tunawa da kalmar data fadawa fk to da ko da uban wa zatayi tunani ya furta hakan a kasan rashi .
kwance take akan bed din ummi Amman ba bacci takeyi ba ,hannuta rike da wani English novel mai suna ,mumy why sanye take cikin kananan kaya, pencil jeans da riga iya gwiwa a natse take karatunta dan tana jin dadi labarin yarinyar ciki litattafin ta birgeta kwaira ,ta yadda take kokarin kwatarwa kanta enci saboda mahaifiyarta ta hanata auren saurayin da take son ..
Cikin isa da kasaita yashigo dakin , tana jin motsen bude kofa Amman tashare dan batason abinda zai katse mata karatunta .Jin kamshin turarensa yasa ta dan dago idanunta suka sauka akansa , ganinsa yasa ta dan mike daga kwanciyar datayi, tasha jinin jikinta bata san meke sata jin yawan faduwar gaba ba, a duk sanda taga yaya DEENi .
ta gaidashi batare daya kalli inda take ba , ya amsa mata a ciki ,km cikin isa da takama sannan a takaice , tamkar dai yadda yasaba dan baya son duk abinda zai sa magana tayi tsawo atsakaninsu .
sai dai ita kam tsintar kanta tayi da zuba masa idanunta, tana binsa da wani irin mayyen kallo , cikakken namiji ne sosai mai ji da kansa , ko a tafiyarsa zaka shida haka. gabadaya bbu wata alamun ragwanta atare dashi .kana ganinsa zakaji ya birgeka ,daman aikin da yakace shi kennan wato jami'in tsaro .Har suka gaisa da ummi dake tsaye fitowarta kennan daga bathroom ya juya da niyar barin dakin, idanun Zeenat na kansa tamkar zata ya dawo ya zauna kada ya fita saboda tsoron masu farautarsa ,takasa dauke idanunta daga kallonsa take taji wani irin masefaffen kishinsa ya diram mata zuciyarta ta dinga rawa bata idanunta a kansa ba sai data daina ganinsa .
Ummi tabita da kallo tausayi tace inkin gama kallon nashi sai ki tashi ki hado masa abinsa ko kawai soyayya aka iya ba'asan tattali ba , Zeenat ta dan turo baki tace ni dai ummi kwanan bansa abinda na miki ba komai nayi sai kin min fada, ki dinga ganin laifina , nifa bashi nake kallo ba , ummi tace eh ai nasan bashi kike kallo ba kuruwarsa kike kallo jairar yarinya kawai ni tashi ban guri .
Washegari
Zeenat tarasa dawa zatayi zance yaya DEENi taji dadi kuma yaba shawara tamkar yadda zuciyarta ta aminta dashi ,ganinta duk wanda ta nufa da maganar baza tasamu goyon baya ba ,kmr dai yadda ummi tayi ,
Maryam ce ta fado mata a rai ,dan haka tashirya taje har part din su.
YOU ARE READING
AUREN SIRRI COMPLETE
Mystery / ThrillerMatar shi ce ta farko bata san haihuwa, idan ta samu ciki sai ta zubar, as ending yake yin auren sirri da mai aikin gidan