💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗AYSHA A BAGUDO
Dedicated to
HAUWA A USMAN
JIDDARHKainuwa association
Page 98
Ki daina furta kalmar mutuwa nan nablah addu'a kawai shine mafuta .
zeenat wacce gabadaya tagama rudewa sbd ganin halin da nablah take ciki tasoma zariya a dakin tana Kai kawo da furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun.
A rude ummi tace kamamin ita zeenat mukaita dakin kasa .Zeenat dake tsintitin acikin dakin takaraso da sauri .
Takai hannuta jikin nablah ita da ummi zasu kamata.
nablah tayi saurin girgiza kanta tana dukan Tear's da tafin hannunta .
kibari akai ki dakin kasa nablah zai fi sauki akan nan din.uhmmmm ummi uhmmmm takasa cewa komai sai uhmmmm da murkususu ciwo .
take wani irin gumi me zafi shiga tsaftsafo mata takoina jikinta.
Jikinta ke wani irin kirma Dan azabar radadin ciwo.
ta dinga cizan lip's dinta da karfi tsabar tashin hankali .
kuka take da idanunta tana kokarin kamo hannu ummi 'aiko Allah yabata sa'a ta damke hannun ummi 'cikin nata da karfi tsiya .
nishi take hankali sbd numfashinta dake sizing yana dawo .
zeenat dibo min ruwa a cup kikawo nayi mata addu'a.hk zeenat ta fita jikinta Na rawa biyu biyu ta dinga taka step taje takawo ummi ruwa acikin cup .
ummi takarba tayi mata addu'a tabawa nablah tasha Amman still ciwon Bai ragu ba .
Sai abunda ya Karu Na naxaba wani irin murdawa cikin nata yayi da karfi aiko ta saki wata irin razananniyar kara wanda Yasa zeenat fashewa da wani irin matsanancin kuka jikinta yacigaba da rawa .
Tana kuka tace ummi Dan girma Allah mukai yarinyar nan asibiti karfa Yar mutane ta mace mana mushiga uku Daga taimako ..bazata mutu ba inshallahu .
Duk wani taimakon da ummi tasan anayiwa me nakuda tayiwa nablah shi Amman Sam bbu wata alamun zuwan bby wanda hkn ya nuna ummi cewa doguwar nakuda gareta.
Daman km dayawa anasamun hk wani zaga alokacin rainon ciki basashan wahala sai gurin haihuwa wasu km tun gurin daukar 'cikin suke shan wahala har zuwa haihuwa wasu ma kwata kwata basu San da wannan matsalar ba zasuyi renon ciki lafiya Haka ma haihuwar 'cikin sauki zasuyi ta .kuka nablah keyi tana kiran mutuwa zatayi itama zeenat kuka take tana cewa ummi kinga abinda nake gudu da jin tsoro ko........
ummi kalli yadda yarinyar mutane ke shan wahala kalli yadda numfashinta keyi ni dai wlh tsoro nake ji wani abu yasameta 'cikin wani irin kuka zeenat takarashe zancenta da wallahi ummi bazan iya haihuwa ba ban zan iya ba wallahi Na hakura da haihuwar gabadaya .'Cikin fushi ummi ta buga mata tsawa Dan Allah kiyiwa mutane shr duk kinbi kin cikawa mutane kunne ba'a haihuwa ke uwarki ta haifeki.
zakizo ki ishi mutane da surutan banza da wofi shasha kawai 'aiko kowace da yadda haihuwa take zuwa mata kamamin ita ni mukaita kasa .. .Haka suka kama nablah zuwa dakin kasa ummi ta kwantar daita tunda tun dazu a tsugunne take a sama har garin Allah yawaye ciwo yaki ci yaki cinyewa banda murkususu ciwo bbu abinda nablah keyi da ikin kiran sunan mamata da mutuwa zatayi .
Wani daren yashigo nablah Na kan abu daya , tayi firifiri daita tayi mugun fita haiyacinta iya jigatuwa tayi shi har tasoma gajiya tana janyo numfashi da kyar tana fitawar da kyar km still ummi da zeenat Na tsaye akanta Amman haihuwa shr.
Gashi km sosai nablah ke jin wata irin azababen azaba har tasoma fezgar gashin kanta ....
ta daina gane suwaye akanta ta dawo bbu karfin komai ajikinta bakinta ya bushe sannan Yayi fari fat.. idanunta suka bushe .
hawayen dake idanunta suka kafe suka bar xuba bakinta ne kawai ke motsin ahankali tana karanto duk wata addu'ar tada iya ji taje da zata iya data fizge 'cikin jikinta ta huta da radadin azabar ciwon datake ji ...
YOU ARE READING
AUREN SIRRI COMPLETE
Mystery / ThrillerMatar shi ce ta farko bata san haihuwa, idan ta samu ciki sai ta zubar, as ending yake yin auren sirri da mai aikin gidan