80

14K 372 7
                                    

💗💗💗💗💗
  AUREN SIRRI
      💖💖💖
💗💗💗💗💗


AYSHA A BAGUDO

      Dedicated to
HAUWA A USMAN
      JIDDARH

Page 100

Nablah ki natsu ki dawo 'cikin haiyacinki muyi mgn 'cikin tsanake da fahimtar juna da farko kin amince da zaki bamu abinda zaki haifa wanda har muka sanyawa rayuwarmu son abinda ke cikinki.
" to meyyasa yanzu kika canza ra'ayinki alhalin duniya tagama sannin wayan nan ya'yan ya'yanmu ne nida matata ?

Ilahirin jikinta da bakinta wara suke gurin cewa  nidai  kawai ji nake a halin yanzu bazan iya kyautar dasu ba.
. saboda kinsha wahala gurin haihuwarsu shiyasa bazaki iya badasu ko me ?
Kai tsaye taji ya 'aiko mata da tmbyr datasa ta tsura masa shanyayyun idanunta da suke cike da ruwan hawaye taki ce masa komai sai kallonsa kawai  take ..
"jikin deeni Yayi sanyi sosai sbd ganin yadda  yanayinta ya sauya . yarasa ta inda zai bullo mata.
ta  kalleshi sosai Yayi matukar bata tausayi  Amman har 'cikin zuciyarta bata jin zata amince tabashi yayanta kyauta .
"  tacigaba da dubansa can km yace kina jina ko kiyi hakuri kibar mana yaran nan nida matata nayi miki alkwarin zan raba tarin dukiya biyu Na baki rabbi akansu kije kicigaba da rayuwarki .
Sosai ta sake  tsareshi da shanyayyun idanunta tamkar zata cinyeshi  tana mishi wani irin kallon rainin wayo.
hakan Yasa gabansa cigaba  da faduwar dayake .
shima kallonta yake yana jira Daga gareta tare da  mamakin canzawarta  a'cikin zuciyarsa .
idan wani ya fada masa zata rikide ta dawo masa Haka wallahi zai rantse da Allah  yace karya ne ranta a matukar bace tace  Kai dukiya ta dama km take rudarka har kake jin Kai wani ne .
Amman ni bbu abinda za'a bani a duniyar nan da zai Saka Na iya kyautar da ya'yana har UKu  ba daya ba.
ko mahaikaciya ce Ni bazan soma yin wannan dayin aikin ba ballanantana Ina 'cikin haiyacina, yakarasa fadar hk tana nuna brain dinta da yatsan hannuta.
kana tacigaba nidai Dan girma Allah Na rokeku daku barmin ya'ya Na Ina sansu nima a duk yadda suke.

deeni ya runtse idanushi gam tare da furta ya Allah akasan zuciyarsa  ....yasoma cizan lips dinsa da karfi .
gabadaya komai Na 'cikin duniyar nan yasoma tsaya masa Bai taba tunani sanadiyar yarinyar zai taba  shiga  'cikin tashin hankali irin Haka ba.
   ya dauka rashin son 'cikin jikinta datake tun farko zai tsaya a Haka ne .
Amman a kalmomin bakinta na yanzu komai ya sauya agareshi yagane  shi din bakomai bane a duniya nan .
sannan ya soma fahimtar Bai isa yace zai ma kaddarsa wayo ba .
Yau din nan tazo masa da tarin abubuwa da daya farinciki dake  tattare da tashin hankali mara misaltuwa .

Shin yanzu ya zaiyi da kaddarar data fada masa ?

Ya'yan da zai fara samu a duniya sunzo masa da wani irin salo  na daban .
yanzu mezai cewa danginsa da yan'uwa ?

Hakika Komai yagama dagule masa ahankali ya juya saitin da zeenat take tsaye surusuru tana aikin barin jiki da marairaice wa .
yana aika mata da wani irin matsiyacin kallo me frigita zuciyar wanda akawa  sannan muryarsa a fusace  yace kinga ni ko ?
Kinga  irin abinda sakacinki  ya haifar mana   ko ?
Me kike tunani zai faru gaba  idan har taki amincewa tabada yaranta ?

Zeenat da jikinta ke mugun kirrrrrrma ta sake fashewa da wani irin matsanancin kuka tana yarfe hannuwa .
  yanzu dakin yi hakuri kin haifi wanda Allah yabaki da duk hk Bai faru ba.
da km baki samu 'cikin tsaka me wuya ba. Amman bbu komai duk 'cikin wannan lamarin ni akafi cuta yakarasa mgnrsa yana jin kunar rai acikin zuciyarsa yayinda kirjinsa ke wani irin buguwa da karfi .
Shi kanshi  kuka yake son yi ko zai daina jin radadin azabar ciwon zuciyarsa keyi .

banda kuka bbu abinda zeenat keyi ita kanta tasan ta cuci kanta da kanta.
Ta  ruguza rayuwarsu sbd  sakacinta  da  son zuciyarta ta Mike Daga inda take  ahankali tana layi ta rungume ummi ajikinta  tana matsanancin kuka.
Ummi kiyi hakuri a rayuwa nasan Na cutar daku Amman ko daidai rana daya ummi baki taba kina ba .
Sai ma sabuwar kulawa da kike bani hakika ke uwace guda har da rabi samun irin Ku ahalin yanzu zai yi wuya  ummi kiyi hakuri abida nayi  ki ya femin Na cutar dake domin ba irin tarbiyya da kika bani ba kennan ta sake tsanata kukanta.
ummi itama ta rungumeta sosai  tana zubda hawayen tausayin diyarta arayuwa ta tsani abinda zai saka zeenat dinta  zubd hawaye matukar tana da yadda zatayi.
kasa cewa komai tayi Sai aikin  rarrashita datake tana shafa bayanta ..

AUREN SIRRI COMPLETE Where stories live. Discover now